Aminiya:
2025-07-25@22:21:39 GMT

Ɓullar Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja

Published: 24th, July 2025 GMT

An samu ɓarkewar cutar amai da gudawa wato kwalara a ƙananan hukumomi shida na Jihar Neja, inda rahotanni suka ce mutum 13 ne suka mutu tare da wasu mutane sama da 236 da ke jinya a asibiti.

An fara samun ɓullar cutar ne a Ƙaramar hukumar Shiroro tun a ranar Lahadin da ta gabata zuwa Ƙananan hukumomin Bosso da Minna da Magama da Bida da Munya, inda jami’an kiwon lafiya suka tabbatar da ƙaruwar ɓullar cutar a ƙananan hukumomin da abin ya shafa.

Jirgin Rasha mai dauke da mutum 50 ya yi hatsari a China Matar aure ta kashe mijinta a kan abinci a Yobe

Majiyoyi sun bayyana cewa, yankunan Chanchaga a Minna da Bosso da Shiroro na daga cikin yankunan da lamarin ya fi ƙamari, lamarin da ya sa gwamnatin jihar ta ɗauki matakin gaggawa na kiwon lafiya.

Kwamishinan lafiya a matakin farko, Dakta Ibrahim Dangana, ya tabbatar da ɓullar cutar, ya kuma ce jihar ta ɗauki matakai da dama domin daƙile yaɗuwar cutar.

A cewarsa, an kafa cibiyoyin kula da lafiya da killace marasa lafiyan a kowace ƙaramar hukumar da abin ya shafa.

Dangana ya ce “Mun kafa cibiyoyin kulawa da killace masu jinya don rage yaɗuwar cutar, kuma muna kuma wayar da kan jama’a kan cutar,” in ji Dangana.

Ya ƙara da cewa, “Shirin wayar da kan jama’a ya shafi Ƙungiyoyin addini irin su Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), kungiyoyin Islama, da masarautu takwas da ke jihar”.

Domin ƙarfafa ƙoƙarin hana yaɗuwar cutar, gwamnatin jihar ta buɗe cibiyar killacewa a tsohon reshen cibiyar kula da lafiya na matakin farko na Marigayi Sanata Idris Ibrahim Kuta daura da tsohon titin filin jirgin sama a Minna.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwalara

এছাড়াও পড়ুন:

UNICEF Ya Bukaci Jihar Kano Ta Bai Wa Yara Muhimmanci A Kasafin Kudi

Asusun Kula da Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya nuna damuwa kan halin da yara ke ciki a jihar Kano, yana mai kira ga gwamnatin jihar da ta ƙara zuba jari a fannin lafiya, ilimi, da abinci mai gina jiki ta hanyar kasafin kuɗi da ya danganci makomar yara.

Shugaban ofishin UNICEF na Kano, Mista Rahma Rihood Muhammad Farah, ya bayyana hakan yayin wani taron tattaunawa da ‘yan jarida kan kasafin kuɗi mai la’akari da bukatun yara, inda ya gabatar da wasu alkalumma masu tayar da hankali dangane da rayuwar yara a jihar.

Farah ya ce jihar Kano na da yara fiye da miliyan 6 da rabi da ke ƙasa da shekaru 18, wadanda da dama daga cikinsu na fuskantar matsaloli masu tsanani kamar mace-macen yara, ƙarancin abinci mai gina jiki, da kuma rashin samun ingantaccen ilimi da kiwon lafiya.

Ya bayyana cewa, bisa ga rahoton MICS na 2021, yara 143,000 na mutuwa kafin su kai shekara biyar, yayin da kusan yara miliyan 2 da 900,000 ba su da cikakken rigakafi, sannan fiye da yara miliyan 4 na rayuwa cikin talauci.

Haka kuma, sama da yara miliyan 2 300,000 da suka kai shekarun makaranta suna zaune a gida ba tare da samun ilimi ba, wani hali da ya ce ya zama wajibi a sauya shi ta hanyar karfafa kasafin kuɗi na kula da yara.

Ya ce duk da wasu sauye-sauye da ake yi, fannin walwalar al’umma a Kano har yanzu na samun ƙarancin kudi, inda ya zargi sauyin kasafi da rashin daidaito a fannonin lafiya, ilimi da kare hakkin yara da janyo cikas ga cigaba.

Farah ya bayyana kasafin kuɗi mai kula da yara a matsayin wata dabara mai mahimmanci, fiye da ware kuɗi kawai ga makarantu da asibitoci.

A nasa jawabin, Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Kano, Hon. Muhammad Bello Butu Butu, ya tabbatar da kudurin majalisar na tabbatar da cikakken aiwatar da kasafin kuɗi ga ma’aikatu da hukumomi.

Sai dai ya soki wasu shugabannin ma’aikatu da hukumomi da rashin kokarin karɓar kuɗaɗen da aka ware musu da kuma gazawar aiwatar da su, duk da kokarin bangaren zartarwa wajen sakin kudin. Ya bayyana cewa kimanin kashi 35% na kasafin kuɗin jihar na zuwa fannin lafiya ne da ilimi.

Masu ruwa da tsaki da suka halarci taron, ciki har da ‘yan jarida, kungiyoyin farar hula, da ma’aikatun gwamnati, sun yi kira ga gwamnatin Kano da ta tabbatar da kasafin kuɗi mai la’akari da yara, ta ƙara yawan kuɗaɗen da ake warewa shirye-shiryen kula da yara, tare da tabbatar da gaskiya da rikon amana a wajen aiwatar da kasafin.

 

Daga Khadijah Aliyu 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja
  • Ruwa da iska sun kashe mutum 5, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Ruwa da iska sun kashe mutum, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan kisan sama da mutum 100
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace
  • Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Bindiga Sama Da 100 A Neja
  • Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan kisan mutum sama da 100
  • Cutar Amai Da Gudawa Ta Hallaka Mutane 13 A Neja
  • UNICEF Ya Bukaci Jihar Kano Ta Bai Wa Yara Muhimmanci A Kasafin Kudi