Nigeria: Zazzabin “Lassa” Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutane 118 Tun Farkon Wannan Shekara
Published: 1st, April 2025 GMT
Cibiyar da take dakile yaduwar cutuka masu yaduwa ( NCDC) ta sanar a ranar Lahadin da ta wuce cewa, a kalla mutane 118 ne su ka rasa rayukansu sanadiyar yaduwar zazzabin Lassa tun daga farkon wannan shekara ta 2025.
A wata sanarwar da cibiyar ta fitar ta bayyana cewa; An sami yaduwar wannan cuta a cikin jahoji 33 na fadin kasar, kuma bincike da aka yi akan wadanda ake tsammanin ta kama, ya tabbatar da cewa an sami mutane 645 da su ka kamu da ita.
Ita dai wannan cutar mai yaduwa a Nigeria, ana kamuwa da ita ne ta hanyar cudanya a tsakanin mutane ko kuma taba kayan gida da su ka gurbana daga bahaya ko fitsari na mutane da su ka kamu da ita.
Tare da cewa an dauki shekara da shekaru ana fama da wannan cutar a cikin kasar ta Nigeria, sai dai har yanzu babu wani ci gaba na azo a gani da aka samu na dakile wannan cuta, saboda halayyar kazanta da rashin muhalli mai tsafta.
Ana samu wadanda suke tsira daga cutar amma a lokaci daya tana kisa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hamas : Ziyarar ministan Isra’ila Ben-Gvir a masallacin al-Aqsa kan iya tayar da yakin addini
Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta yi Allah wadai da kutsawa cikin masallacin al-Aqsa da ministan Isra’ila Itamar Ben-Gvir ya yi a baya bayan nan, tana mai cewa tana da nufin tayar da “yakin addini” a wannan wuri mai tsarki.
A cikin wata sanarwa da ta fitar, Hamas ta ce “Kutsen da Itamar Ben-Gvir, ya yi a cikin masallacin Al-Aqsa mai alfarma, da kuma ziyarar tsokanar da ya kai a harabar masallacin… rashin mutunta ra’ayin musulmi da kuma keta alfarma da matsayin masallacin Al-Aqsa a duniyar Musulunci.”
Kungiyar ta jaddada cewa wannan wulakanci da aka yi yana nuna ” girman kai na wannan gwamnati mai tsattsauran ra’ayi da kuma dagewarta na rura wutar yakin addini.”
Hamas ta kuma bukaci dukkanin kasashen Larabawa da na musulmi masu son ‘yanci da su kare masallacin Al-Aqsa daga fuskantar karuwar kutse.
Ministan na Isra’ila Ben-Gvir tare da wasu gungun ‘yan Isra’ila sun mamaye harabar masallacin Al-Aqsa da ke gabashin Quds da aka mamaye tare da gudanar da ayyukan ibada a harabar masallacin.