Tawagar kwararru daga hukumar makamashin Nukliya IAEA zata ziyarci kasar Iran nan ba da daewa ba.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Kazem Gharibabadi mataimakin ministan harkokin wajen kasar a bangaren sharia da kuma harkokin kasashen waje ne ya bayyana haka.

Ya kuma kara da cewa tawagar zata tattauna da Jami’an gwamnatin kasar Iran kan yadda mu’amalar hukumar zata kasance da Iran.

  Gharibabadi ya bayyana cewa idan kasashen yamma sun yi kokarin amfani da shrin SnapBack na yarjeniyar JCPOA zasu gamu da maida martani mai tsanani, sannan ya kara da cewa mu’amala da hukumar IAEA da kasar Iran zata sauka saboda amfani da karfi kan cibiyoyin nukliyar kasar Iran wanda Amurka da HKI suka yi a kallafeffen yaki na kwanaki 12 a cikin watan yunin da ya gabata.

Mataimakin ministan ya bayyana cewa, Iran zata ci gaba da kasancewa cikin yarjeniyar NPT mai hana yaduwar makaman nukliya a duniya. Amma dokar da Majalisar dokokin kasar Iran ta kafa ta jingine hulda da hukumar IAEA ya sa Iran za ta sanya hulda da hukumar takaitacce shi dimma tare da wasu sharudda guda biyu.  Gharib abada ya fadawa yan jaridu a birnin NewYork a ranar Laraban da ta gabata kan cewa tawagar ba zata kai ziyara cibiyoyin makamashin nukliya na kasar ba. Sannan ya kammala da cewa hukumar makamashin nukliya na kasar Iran na lissafin irin asarorin da hare-hare Amurka suka yiwa cibiyoyin Nuklkiyar nkasar A Esfahan, Natansa da kuma Fordo.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Trump ya fitar da Amurka daga UNESCO saboda amincewa da  Falasdinu a matsayin Mamba

Amurka ta yanke shawarar ficewa daga hukumar kula da ilimi da kimiya da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya UNESCO a karo na biyu saboda matakin da ta dauka na shigar da Falasdinu a matsayin mamba.

Mataimakiyar sakatariyar yada labaran fadar White House Anna Kelly ta sanar da matakin a cikin wata sanarwa a ranar Talata.

Kelly ta ce dalilin da ya suka dauki wannan kan hukumar UNESCO, shi ne ta tallafa wa shirye-shiryen da Amurka ke kallonsu a matsayin wadanda ba su dace da muradunta ba.

“Shugaba Trump ya yanke shawarar janye Amurka daga UNESCO, wadda  ke kula da ayyuka a bangaren raya al’adu da ilimi da zamantakewar al’umma, saboda daukar wau matakai  wadanda ba su dace da manufofin Amurka ba,” in ji Kelly.

Ta ci gaba da cewa, shigar da Falasdinu a matsayin mamba a hukumar UNESCO, Amurka na Kallon hakan a matsayin babbar  matsala kuma ya saba wa manufofin Amurka, wanda hakan ke ke kara haifar da karuwar kalaman kyama ga Isra’ila a cikin kungiyar.

Darakta-janar na UNESCO, Audrey Azoulay, ya bayyana matukar Rashin jin dadinsa kan matakin da Trump ya dauka na ficewa daga kungiyar, amma ya kara da cewa dama tuni aka yi hasashen haka, kuma UNESCO ta shirya ma hakan, tare da yin nuni da cewa hukumar ta dauki matakin karkata hanyoyin samar da kudadenta, inda kusan kashi 8% na kasafin kudin ta ke fiowa  daga Washington.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Da Eu Sun Fara Tattaunawa A Istambul
  • Faransa Zata Bayyana Amincewa Da Samuwar kasar falasdinu
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jaddada Aniyar Iran Ta Ci Gaba Da Inganta Sinadarin Uranium
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: Taro Tsakanin Iran Da Tawagar Kasashen Turai Dama Ce Ta Gyarar Tunanin Tarai
  • Yan Majalisar Dokokin Kasashen Iran Da Iraki Sun Amince Da Ra’yin Ficewar Sojojin Amurka Daga Iraki
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Hakkinta Na Tace Sinadarin Uranium A Cikin Kasarta
  • Babban Hafsan Sojin Iran Ya Ce: Iran Zata Sanya Duk Wanda Ya Dauki Matakin Wuce Gona Kanta Nadama
  • Pezeshkian: Tunanin Kawo Karshen Shirin Nukiliyar Iran Ya Yi Kama Da Tabuwa
  • Trump ya fitar da Amurka daga UNESCO saboda amincewa da  Falasdinu a matsayin Mamba