Aminiya:
2025-11-02@18:11:14 GMT

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace

Published: 24th, July 2025 GMT

Dakarun Sojin Najeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Ƙananan Hukumomin Rijau da Mariga a Jihar Neja.

’Yan ta’addan sun fito ne daga Jihar Zamfara, yayin da suke tafiya a kan babura ɗauke da muggan makamai.

Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan kisan mutum sama da 100 Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na ƙasa

Sojoji tare da taimakon jiragen yaƙi na sama sun kai farmaki bayan samun bayanan sirri.

Aƙalla ’yan ta’adda 95 aka kashe a yayin artabun.

Sojojin sun kuma lalata babura 18 tare da ƙwato bindigogi kirar AK-47.

Sai dai an yi rashin sa’a soja guda ɗaya ya rasa ransa a yayin fafatawar.

Dakarun sun sake kai wani farmaki na biyu inda suka ƙwato makamai da yawa tare da tarwatsa ’yan ta’addan.

Jama’a daga Warari, Rijau, da wasu ƙauyuka sun yi murnar nasarar sojojin suka samu.

Da yawa daga cikin mazauna yankunan sun tsere daga gidajensu saboda tsoro, amma sun dawo bayan ganin ƙoƙarin da sojoji suka yi.

A wani faifan bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta, an ga yadda jama’a ke taya sojoji murna da godiya.

Wani mazaunin yankin ya tabbatar da cewa farmakin sojojin ya daƙile shirin kai hare-hare da ’yan ta’addan suka yi.

Wani mazaunin yankin shi ma ya ce ’yan ta’addan na shirin kai hari wasu ƙauyuka a Mariga, amma sun gudu bayan farmakin sojoji.

An kama tsohon kansila kan iƙirarin mallakar shanu

A gefe guda kuma, jami’an tsaro sun kama tsohon kansilan Rijau, Mamman Wazo, bisa zargin iƙirarin mallakar shanun da aka ƙwato daga hannun ‘yan ta’adda.

Wata ƙungiyar sa-kai ce ta kama shi tare da abokin aikinsa, kuma aka miƙa su ga ’yan sanda.

’Yan sanda sun ce an samu shanun ne daga yankin Rijau bayan wasu hare-hare da aka kai.

Sojoji sun ceto mutum 138 da aka sace

A wani samame na daban daban, sojoji sun ceto mutum 138 da aka sace a Jihohin Zamfara, Borno, da Adamawa.

Mafi yawan waɗanda aka ceto mata da ƙananan yara ne.

An kuma kama wasu mutane da ake zargin suna taimaka wa ‘yan ta’adda da kayan aiki.

A Jihohin Borno da Adamawa kuma, sojoji sun kama abubuwan fashewa da sauran makamai yayin da suka daƙile wasu hare-haren ’yan ta’addan.

Rundunar sojin ta ce za ta ci gaba da kasancewa cikin shiri don kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Sojoji sun gode wa al’umma bisa goyon bayan da suke bayarwa, kuma sun buƙaci mutane su ci gaba da bai wa hukumomi bayanai masu amfani.

Sun tabbatar da cewa za su ci gaba da kare ƙasar nan daga barazanar ta’addanci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan ta adda Adamawa Artabu dakaru Farmaki yaƙi Zamfara yan ta addan yan ta adda

এছাড়াও পড়ুন:

An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku

’Yan sanda a jihar Legas sun kama wani tsohon fursuna tare da wasu mutum biyu bisa zargin hannu a jerin laifukan fashi da yankan aljihu a jihar kwana biyar da fitowa daga kurkuku.

Tsohon fursunan mai shekaru 25 da haihuwa, Segun Kolawole, an kama shi ne bayan kwana biyar da aka sako shi daga cibiyar gyaran hali ta Kirikiri, a jihar Legas.

Ana zargin ɗa da kashe mahaifinsa a Kano saboda hana shi ƙara aure Juventus ta ɗauki tsohon kociyan Italiya, Luciano Spalleti

Sauran wadanda aka kama tare da shi sun haɗa da Sodiq Isa mai shekaru 27 da Adekanmbi Ganiu mai shekaru 21.

Rahotanni sun nuna cewa an kama waɗanda ake zargin ne bisa laifukan yankan aljihun mutane da sauran laifukan sata a sassa daban-daban na jihar.

Mai magana da yawun ’yan sandan jihar, SP Abimbola Adebisi, ta tabbatar da cafke Kolawole, inda ta ce an kama shi da misalin ƙarfe 8 na safiyar Talata a kasuwar Oshodi, bayan jami’ai sun lura da motsinsa da ya zama abin zargi.

Adebisi ta ce an same shi da tsabar kuɗi ₦80,000 da wayar Infinix Note 40 Pro, waɗanda aka gano daga wani fashi da ya aikata a Opebi, inda ake zargin ya saci ₦200,000 da wayar daga hannun wani ɗan kasuwa da ke barci.

“Bincike ya ƙara tabbatar da cewa ya riga ya sayi sabbin kaya da takalma da wani ɓangare na kuɗin da ya sata, waɗanda suma aka kwato su daga hannunsa,” in ji ta.

Haka kuma, a wani samame daban da aka gudanar da misalin ƙarfe 5 na yamma a ranar Juma’a, jami’an RRS sun kama Sodiq Isa da Adekanmbi Ganiu bisa zargin yunkurin satar wayoyin hannu daga hannun fasinjoji a sassa daban-daban na Legas.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano
  • Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano
  • ’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi
  • Sudan Ta Yi Kira Ga Kwamitin Tsaro Da Ya Ayyana RSF A Matsayin Kungiyar ‘Yan Ta’adda
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Kutsen Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • Shugaban Lebanon Ya Umarci Sojoji Da Su Fuskanci Duk Wani Kutse Na Isra’ila A Kudancin Kasar
  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Ɗaya, Sun Kama Mace Da Zargin Garkuwa Da Mutane A Dajin Kwara