Naira: Kotu ta yanke wa Hamisu Breaker da G-Fresh hukunci ɗaurin wata 5
Published: 25th, July 2025 GMT
Kotun Tarayya da ke zamanta a Jihar Kano, ta bayar ta yanke wa fitaccen ɗan Tiktok, Al-Ameen G-Fresh da mawaƙi Hamisu Breaker, hukuncin ɗaurin wata biyar a gidan yari bayan samun su da laifin wulaƙanta takardun Naira.
Mai shari’a S.M. Shuaibu ne ya yanke hukunci, inda ya yi musu ɗaurin wata biyar a gidan yari, bayan sun amsa laifin da ake tuhumarsu a gaban kotu.
Hukuncin ya biyo bayan tuhumar da Hukumar EFCC ta shigar da su a gaban kotu, bisa laifin wulaƙanta Naira.
A cewar ƙarar, G-Fresh ya watsa kuma ya taka takardun Naira 1,000 har na Naira 14,000 yayin da yake rawa a shagon wata mai suna Rahma Sa’idu a Ƙaramar Hukumar Tarauni.
Shi kuma Hamisu Breaker, ya watsa Naira 30,000 na takardun Naira 200 a wani taron walima da aka yi a Hadeja da ke Jihar Jigawa.
Dukkaninsu sun aikata laifin ne a watan Nuwamban 2024.
Laifin ya ci karo da Sashe na 21(1) na dokar Babban Bankin Najeriya (CBN) ta shekarar 2007, wadda ta haramta cin zarafi ko wulaƙanta Naira.
Bayan amsa laifinsu, kotun ta ba su damar biyan tara maimakon zaman gidan yari.
Kowannensu ya biya tarar Naira 200,000, wanda hakan ya sa aka sake su bayan tsare su.
Wannan hukunci na nuna cewa gwamnati na ɗaukar wulaƙanta Naira a matsayin babban laifi, duk da cewar akwai damar samun beli ko biyan tara.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Mawaƙi Wulakanta Naira
এছাড়াও পড়ুন:
‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8
Kwamitin ya nemi a mayar da sama da Naira miliyan 124, kusan dala 795,000 zuwa asusun gwamnatin tarayya, an kuma bayar da karin wasu kudade da suka hada da Naira miliyan 31.7 da dala 155,923.00, a matsayin wadanda aka kashe ba bisa ka’ida ba.
An umarci ma’aikatar da ta kwato Naira miliyan 49.4 da aka biya, domin yin gyaran ba tare da bin ka’idojin sayen kayayyakin ba. Kazalika, an raba Naira miliyan 9.2 ga jami’an ofishin jakadancin, ba tare da cikakkiyar shaida ba.
Haka nan kuma, an binciki bankin noma; kan basussuka kimanin Naira biliyan 75.6.
Kwamitin ya umarci hukumar da ta buga jerin sunayen wadanda ake bi bashi a akalla a jaridu guda uku na wannan kasa tare da yin kira ga hukumomin yaki da cin hanci da rashawar da su kwato wadannan makudan kudade.
Haka nan, dole ne a kwato karin Naira miliyan 350; kana kuma a gabatar da shedu cikin kwanaki 90.
Sannan, an umarci hukumar kula da gidajen yari ta Nijeriya da ta dawo tare da tura Naira miliyan 7.47 na harajin da ba ta biya ba.
Haka zalika, an umarci hukumar kula da fitar da kayayyaki ta Nijeriya (NEPZA), da ta kwaso motoci takwas na hukumar tare da tabbatar da dawo da guda hudu da ma’aikatar masana’antu, kasuwanci da zuba jari ta rike ba bisa ka’ida ba.
An kuma bayyana (NEPZA) da laifin karkatar da sama da Naira miliyan 12 tare da sanya takunkumi ga jami’in da kula da harkokin kudi.
An gurfanar da Karamar Hukumar Kwali da ke babban birnin tarayya gaban kuliya, bisa zargin biyan kudi kimanin Naira miliyan 82 da aka raba wasu mutane su 105 da ba a san ko su wane ne ba.
Kazalika, an bukaci tsohon shugaban majalisa day a dawo da kudade zuwa asusun gwamnatin tarayya tare da wasu shaidun day a mika wa kwamitin.
Haka nan, an umarci hukumar kwastam ta Nijeriya da ta yi aiki tare da Akanta Janar na Tarayya, domin samar da cikakken jerin dukkannin abubuwan da aka bai wa asusun tarayya da wadanda ban a tarayya, don tabbatar da hakikanin kudaden da ake da su.
A hukumar samar da wutar lantarki ta karkara kuma, an bankado badakalar kudi sama da Naira biliyan 1.3.
Haka nan, an umarci tsohon manajan darakta da ya mayar da Naira miliyan 394 da ya batar kan ayyukan wutar lantarki da hukumar tattalin arziki ta kasa ta amince da shi.
Bugu da kari, akwai kuma kudaden da suka hada da Naira miliyan 4.2 da aka kashe wajen aiwatar da tallace-tallace, ba a kan ka’ida bad a kuma canza Naira miliyan 969 zuwa Yuro, shi ma ba a kan ka’ida ba, tare kuma da ba da shawarar daukar matakan ladabtarwa ga jami’an da ked a alhakin gudanar da ayyukansu.
An samu kungiya kula da dabbobi ta Nijeriya da badakalar kudaden haraji na duti da kuma sauran kudaden haraji da suke karba.
An bai wa kungiyar umarnin dawo da Naira miliyan 1.1 na harajin dutin daga hannun ‘yan kwangila tare da kuma dawo da sama da Naira miliyan 19 na wasu kudade.
Yayin da majalisa ke karbar rahoton kwamitin, ta yi kira ga hukumomin yaki da cin hanci da rashawa daban-daban da suka hada da EFCC, ICPC da FIRS da su kwato wadannan kudade.
Kwamitin ya kuma kara jaddada bukatar gaggauta bai wa shugabannin hukumomi damar nada masu binciken kudi daga waje, inda kuma ya bayar da shawarwarin yin gyara ga ka’idojin kudi ko wata takardar da sakataren gwamnatin tarayya zai bayar.
Mataimakin kakakin kajalisar, Rt. Hon. Benjamin Kalu, wanda ya jagoranci zaman majalisar tare da sauran ‘yan majalisa, sun yaba wad an majalisa Salam da sauran ‘yan kwamitin, bisa ga kwazon da suka nuna wajen samar da wannan cikakken rahoto.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp