Leadership News Hausa:
2025-07-25@21:51:53 GMT

Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

Published: 24th, July 2025 GMT

Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

An cimma matsaya kan zaɓensa bayan wata ganawa da aka yi a Abuja tsakanin Shugaba Bola Tinubu da gwamnonin APC.

Ana sa ran manyan shugabannin jam’iyyar za su tabbatar da naɗinsa a yau Alhamis.

Farfesa Yilwatda, ya fito ne daga Jihar Filato da ke yankin Arewa ta Tsakiya, yankin da suke da alhakin riƙe kujerar shugabancin jam’iyyar.

Wasu daga cikin ‘ya’yan jam’iyyar sun ce kasancewarsa Kirista zai taimaka wajen daidaita shugabanci, duba da cewa shugaban ƙasa da mataimakinsa Musulmai ne.

Shugabannin jam’iyyar na fatan Farfesa Yilwatda zai kawo sabon salo, tare da haɗa kan jam’iyyar kafin tunkarar zaɓe mai zuwa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Farfesa Yilwatda

এছাড়াও পড়ুন:

Al’ummar Fegin Mahe Sun Yi Zanga-zanga Kan Kisan Jama’a Da ‘Yan Bindiga Ke Yi

Daruruwan mazauna kauyen Fegin Mahe da ke yankin Ruwan Bore a karamar hukumar Gusau ta Jihar Zamfara, sun gudanar da zanga-zanga a gaban Gidan Gwamnati da ke Gusau, inda suka bukaci gwamnatin jihar ta dauki matakin gaggawa kan kisan gilla da ‘yan bindiga ke yi a yankinsu.

Masu zanga-zangar sun rike takardu masu dauke da rubuce-rubuce kamar su: “Muna bukatar zaman lafiya a yankunanmu” da “Gwamnati ta cika alkawarin da ta dauka”.

A cewar mazauna kauyen, harin ya faru ne da safiyar ranar Laraba, lokacin da wasu ‘yan bindiga dauke da manyan makamai suka afka wa kauyen, inda suka rika harbin mai-kan-uwa-da-wabi.

Al’ummar yankin sun bayyana harin a matsayin daya daga cikin mafi muni da suka taba fuskanta a ‘yan shekarun nan, wanda ya bar su cikin tsoro da fargaba.

Masu zanga-zangar sun ce manufarsu ita ce jawo hankalin gwamnati kan tabarbarewar tsaro a yankin da kuma bukatar daukar matakin gaggawa don dakile kisan fararen hula da ake ta yi ba kakkautawa.

Sun kuma koka da cewa har yanzu akwai gawarwakin wasu daga cikin mutanen da aka kashe a dajin, amma babu wanda ke iya dauko su saboda tsoron sake fuskantar hari  daga hannun ‘yan bindigar.

Har zuwa lokacin da ake hada wannan rahoto, ba a samu wata sanarwa ko martani daga gwamnatin jihar ba dangane da harin ko kuma zanga-zangar da aka gudanar.

 

Daga Aminu Dalhatu

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Masu Neman Takarar Shugaban Kasa A PDP Sun Kara Matsa Kaimi Bayan Ficewar Atiku
  • Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
  • HOTUNA: Yadda Kwankwaso ya karɓi ’yan APC zuwa NNPP a Kano
  • An kashe mata da yara a sabon harin Filato
  • Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda
  • An rantsar da Nentawe sabon shugaban APC na ƙasa
  • Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na kasa
  • Al’ummar Fegin Mahe Sun Yi Zanga-zanga Kan Kisan Jama’a Da ‘Yan Bindiga Ke Yi
  • Tinubu Ya Gana Da Gwamnonin APC Gabanin Taron Jam’iyyar