Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan
Published: 28th, July 2025 GMT
Shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama’ar kasar Sin, Zhao Leji, ya kai ziyarar sada zumunta a kasar Kyrgyzstan daga ranar 23 zuwa 24 ga wata, inda ya gana da shugaban kasar Kyrgyzstan Sadyr Nurgozhoevich Japarov a birnin Bishkek.
Yayin ganawarsa da Japarov, Zhao Leji ya bayyana cewa, kasar Sin tana son yin hadin gwiwa tare da kasashen tsakiyar Asiya ciki har da Kyrgyzstan, don inganta gina al’umma mai makoma bai daya tsakanin Sin da kasashen tsakiyar Asiya.
Japarov ya bayyana cewa, layin dogo tsakanin Sin da Kyrgyzstan da Uzbekistan, ba wai wata muhimmiyar hanyar sufuri ce kadai ba, har ma wata “hanyar abokantaka” ce dake sa kaimi ga bunkasar tattalin arzikin yankin.(Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
IMF na Shirin aikewa da wata tawaga zuwa Senegal domin tattauna batun basussukan kaaar
Asusun ba da lamuni na duniya IMF ya fada a wannan alhamis cewa yana shirin aikewa da tawaga zuwa kasar Senegal a cikin watan Augusta domin tattauna yadda aza magance matsalar basussukan da ke kan kasar da kuma fara tattaunawa kan tsarin sabon shirin lamuni.
Kasar Senegal na fama da bashin biliyoyin daloli da gwamnatin da ta shude ta karba, lamarin da ya sanya asusun lamuni na duniya IMF ya dakatar da shirin ba da lamuni ga kasar.
A nasa bangaren kuma, wani mai magana da yawun IMF ya ce, “Asusun na bukatar karin bayanai kafin ya karfafa kimanta halin da ake ciki na basussukan kasar Senegal, sannan yana bukatar yarjejeniya kan muhimman matakan gyara.”
Ya kara da cewa, “Da zarar mun cimma matsaya kan manyan matakan gyara, hukumar ta IMF za ta sake yin nazari kan batun, yana mai bayyana cewa “zai yiwu a cimma matsaya kan wadannan matakan nan da makonni masu zuwa.”
Kakakin ya kara da cewa “Hukumar lamuni ta duniya IMF ta yi kiyasi bisa ga sabbin bayanai daga hukumomin kasar Senegal cewa basusukan da aka boye wanda gwamnatin da ta gabata ta karb, sun kai dala biliyan 11.3 a karshen shekarar 2023. Wannan ya hada da wani kaso na bashin kamfanonin gwamnati da aka kiyasta kusan kashi 7.4% na GDP.”
Kakakin IMF ya ce zai ba da bayanai ga hukumar kan yadda lamarin ya faru , yana mai cewa “IMF na gudanar da bincike na cikin gida da tantancewa a matsayin wani bangare na rashin bayar da rahotonni da suka dace.”