Gwamnatin Jigawa Za Ta Kashe Naira Biliyan 3.5 Wajen Gina Shaguna A Farm Centre
Published: 25th, July 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Jigawa ta fara aikin gina shaguna guda dubu daya a cibiyar kasuwanci ta Farm Centre da ke Kano, wanda zai lakume kudi Naira Biliyan Uku da rabi (N3.5bn), domin bunkasa kudaden shiga na cikin gida na jihar.
Shugaban Kungiyar Hadaka kan Tsaro, Zaman Lafiya da Warware Rikice-rikice a Jihar Jigawa, Muhammad Musbahu Basirka, ne ya bayyana hakan yayin da yake ganawa da manema labarai a sakatariyar NUJ da ke Dutse, babban birnin jihar.
Ya bayyana cewa, hukumar EFCC ce ta mika filin hannun gwamnatin jihar Jigawa a matsayin wani bangare na dawo da kadarorin da jihar ta gada daga tsohuwar jihar Kano.
Ya ce: “Wannan fili da ke a tsakiyar birnin Kano, na daga cikin kadarorin da jihar Jigawa ta gada bisa tsarin raba kadarori da filaye da aka yi bayan kirkar jihar Jigawa daga tsohuwar jihar Kano a watan Agustan 1991.”
“Bayan tattaunawa da masana, shugabannin al’umma da kuma masu ruwa da tsaki, muna sanar da jama’ar jihar Jigawa cewa gwamnatinmu ta yanke shawarar amfani da wannan fili mai muhimmanci domin amfanar kowa da kowa.”
“Manufar ita ce kara habaka kudaden shiga na cikin gida na jihar, kasancewar filin na dag cikin muhimman wuraren kasuwanci na Kano. Gwamnatinmu na fuskantar bukatar fadada hanyoyin samun kudaden shiga ba tare da dogaro kacokan ga kasafin kudi na kasa”.
Yayin da ya ke kira ga ‘yan asalin jihar da sauran mazauna da su rungumi wannan cigaba da fahimta da hadin kai, Musbahu Basirka ya ja hankalin jama’a da a guji siyasantar da wannan lamarin.
“Duk da haka muna maraba da shawarwari masu amfani kan hanyoyin da za a fi amfana da wannan aiki mai matukar muhimmanci domin dorewar ci gaba ga al’umma.” In ji shi.
“Mu a matsayinmu na wakilan kungiyoyin fararen hula, za mu kasance cikin tsaka-tsaki wajen sa ido da tabbatar da cewa an yi aiki mai inganci, tare da yin nazari lokaci-lokaci domin tabbatar da gaskiya da adalci ” in ji Basirka.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Farm Centre Jigawa jihar Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
An kashe mata da yara a sabon harin Filato
Aƙalla mutum 14; ciki har da mata da ƙananan yara ƙanana ne, suka rasu a wani sabon hari da aka kai a Jihar Filato.
Harin ya faru ne da yammacin ranar Alhamis a Gundumar Mangor da ke Ƙaramar Hukumar Bokkos.
Sarkin Katsinan Gusau ya rasu Yadda aka mayar da yaran da aka sace a Kano masu wanke-wanke a KuduWaɗanda aka kashe suna kan hanyarsu ta dawowa daga kasuwar mako-mako da ke garin Bokkos, lokacin da wasu ’yan bindiga suka buɗe musu wuta.
Wannan hari na zuwa ne wata guda bayan wani hari da aka kai wa wasu ‘yan ɗaurin aure daga Zariya a Jihar Filato, inda aka kashe su.
Ƙungiyar Bokkos Cultural Development Forum (BCDF), ta tabbatar da faruwar harin.
Shugaban ƙungiyar, Farmasum Fuddang, ya ce suna jimami da ɓacin rai saboda wannan hari, musamman ganin cewa an sha gudanar da zaman sulhu tsakanin manoma da makiyaya.
Ya ƙara da cewa mata da ƙananan yara na daga cikin waɗanda suka rasu.
Fuddang, ya danganta harin da wata ƙabila.
Ya kuma ce wata ƙungiyar ta’addanci tana ƙone ƙauyuka da ƙwace gonaki a yankin Mushere.
A cewarsa, burinsu shi ne su mamaye dukkanin Ƙaramar Hukumar Bokkos, wadda ta ke hedikwatar noman dankalin turawa a Najeriya.
Sai dai makiyaya a yankin sun ce ba su da hannu a cikin harin.
Shugaban Gan Allah Fulani Development Association (GAFDAN) na yankin, Saleh Adamu, ya karyata zargin, inda ya bayyana cewa babu wata shaida da ke nuna cewa Fulani ne suka kai harin.
Ya ce ba a kama ko mutum ɗaya daga cikin makiyaya a wajen da harin ya auku ba, kuma ya ce wannan zargi sabon abu ne da bai taɓa faruwa a yankin ba.
Saleh ya ƙara da cewa, “A duk lokacin da wani abu ya faru, jami’an tsaro su kan gudanar da bincike kafin a gano waɗanda suka aikata laifin. Muna Allah-wadai da wannan hari baki ɗaya.
“Kisan mutane marasa laifi ba shi da wani uzuri da za a aminta da shi.”
A halin yanzu, jami’an tsaro ba su fitar da wata sanarwa dangane da harin ba.
Wakilinmu ya tuntuɓi jami’an hulɗa da jama’a na Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, da na rundunar ’yan sandan jihar, DSP Alabo Alfred, amma ba su ce komai ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.