Yawan Mutanen Da Suka Rayukansu A Rikicin Lardin Suwaida Na Kasar Siriya Ya Kai 1,400
Published: 26th, July 2025 GMT
Kungiyar da ke sa ido kan kare hakkin bil adama ta Siriya ta tattara bayanan mutuwar mutane 1,400 a loardin Sweida na Siriya
Siriya, Faransa da Amurka sun sanar da wata taswirar hadin gwiwa don tabbatar da zaman lafiya a Siriya, bayan tattaunawar da ba a taba ganin irinta ba a birnin Paris na Faransa, wadda ta hada ministan harkokin wajen gwamnatin rikon kwarya na Siriya Asaad al-Sheibani, da takwaransa na Faransa Jean-Noel Barrot da manzon Amurka na musamman a Siriya Tom Barrack.
Sanarwar ta hadin gwiwa da aka fitar bayan taron na bangarorin uku, ta tabbatar da goyon bayan shirin mika mulki ga gwamnatin kasar Siriya da karfafa hadin kan al’umma, musamman a birnin Sweida da ke arewa maso gabashin kasar Siriya, da hadin gwiwa wajen yaki da ta’addanci, da tabbatar da cewa babu wata jam’iyya da za ta kawo barazana ga zaman lafiyar yankin.
Wakilin Amurka na musamman a Siriya Tom Barak ya bayyana tattaunawar ta Paris a matsayin wani abin koyi na diflomasiyya mai tsauri da ke kawo karshen rikice-rikice, yana mai jaddada cewa kasarsa za ta ci gaba da hada kai da kawayenta wajen gina Siriya mai tsaro da hadin kai.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Brazil Ta Shiga Yaki Da HKI, Inda Ta Kudurin Anniyar Goyon bayan Afirka Ta Kudu A Kotun ICJ
Gwamnatin kasar Brazil tana shirin bayyana goyon bayanta ga Afirka ta kudu a karar da ta shigar a gaban kotun ICJ dangane da tuhumar jami’an gwamnatin HKI da aikaya kisan kiyashi a Gaza.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta nakalto wata jaridar kasar Brazil Folha De S tana fadar haka. Sannan kamfanin dillancin labaran reuters ya tabbatar da labarin a jiya Laraba.
A shekara ta 2023 ne gwamnatin Afirka ta kudu ta shigar da karar don tabbatar da cewa gwamnatin HKI ta na aikata kissan kare dangi kan kasar Amurka. Wanda ya sabawa dokar hana kissan kare dangi ta MDD ta shekara 1948.
Sannan a cikin watan Octoban da ya gabata ne, Pretoria ta gabatar da shaidu da bayanai da suke tabbatar da ikrarinta a gaban alkalan kotun a birnin Hague cibiyar kotun. Wannan ya sa kotun ta fidda sammacin kama firai ministan HKI Benyamin Natanyahu da kuma ministansa na yaki a lokacin Aut galant.
Kasashen duniya da dama sun amince da sammacin, sun kuma dauki alkawalin kama so a duk lokacinda suka kuskura suka shiga kasashensu.