Wulaƙanta Naira: Kotu ta bayar da belin Hamisu Breaker da G-Fresh
Published: 25th, July 2025 GMT
Kotun Tarayya da ke zamanta a Jihar Kano, ta bayar da belin fitaccen ɗan Tiktok, Al-Ameen G-Fresh da mawaƙi Hamisu Breaker, bayan samun su da laifin wulaƙanta takardun Naira.
Mai shari’a S.M. Shuaibu ne ya yanke hukunci, inda ya yi musu ɗaurin wata biyar a gidan yari, bayan sun amsa laifin da ake tuhumarsu a gaban kotu.
Hukuncin ya biyo bayan tuhumar da Hukumar EFCC ta shigar da su a gaban kotu, bisa laifin wulaƙanta Naira.
A cewar ƙarar, G-Fresh ya watsa kuma ya taka takardun Naira 1,000 har na Naira 14,000 yayin da yake rawa a shagon wata mai suna Rahma Sa’idu a Ƙaramar Hukumar Tarauni.
Shi kuma Hamisu Breaker, ya watsa Naira 30,000 na takardun Naira 200 a wani taron walima da aka yi a Hadeja da ke Jihar Jigawa.
Dukkaninsu sun aikata laifin ne a watan Nuwamban 2024.
Laifin ya ci karo da Sashe na 21(1) na dokar Babban Bankin Najeriya (CBN) ta shekarar 2007, wadda ta haramta cin zarafi ko wulaƙanta Naira.
Bayan amsa laifinsu, kotun ta ba su damar biyan tara maimakon zaman gidan yari.
Kowannensu ya biya tarar Naira 200,000, wanda hakan ya sa aka sake su bayan tsare su.
Wannan hukunci na nuna cewa gwamnati na ɗaukar wulaƙanta Naira a matsayin babban laifi, duk da cewar akwai damar samun beli ko biyan tara.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Mawaƙi Wulakanta Naira wulaƙanta Naira
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisa Ta Ba Wa Shugaban NNPCL Awa 24 Ya Bayyana Gabanta Ko Ta Sa A Kamo Shi
Sai dai Sanatoci sun yi watsi da bayanin, inda suka zargi Ojulari da yin watsi da Majalisar. Kwamitin yana binciken tambayoyin tantancewa daga shekarar 2017 zuwa 2023, wanda ya nuna sabanin da ya kai Naira tiriliyan 210, ciki har da bashin da ba a tabbatar da shi ba na Naira tiriliyan 103. ‘Yan majalisar sun firgita cewa Naira tiriliyan 3 zuwa 5 ne kawai aka rubuta a cikin asusun ribar da kamfanin ya samu a cikin shekaru shida.
“Wannan gayyatar ba tilas bace,” in ji Wadada. Ya kara da cewa kwamitin ba yana zargin hukumar ta NNPC da laifin sata bane amma ya jaddada cewa girman sabanin ya bukaci a yi karin haske kai tsaye. Ya bayyana rashin bayyanar Ojulari a matsayin “Cin mutunci” ga kwamitin da ‘yan Nijeriya, ya kara da cewa amincewa da jama’a ga NNPCL ya dogara ne akan gaskiya.
‘Yan majalisar sun bayyana bacin ransu kan rashin zuwan GCEO akai-akai. Sanata Bictor Umeh ya yarda cewa kiran shugaban kasa na iya tabbatar da rashin zuwan Ojulari na baya-bayan nan amma ya yi gargadi game da amfani da Shugaba Tinubu a matsayin garkuwa daga bin doka da oda. “Kada a bar wannan uzurin ya ci gaba.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp