Aminiya:
2025-09-17@22:36:19 GMT

Wulaƙanta Naira: Kotu ta bayar da belin Hamisu Breaker da G-Fresh

Published: 25th, July 2025 GMT

Kotun Tarayya da ke zamanta a Jihar Kano, ta bayar da belin fitaccen ɗan Tiktok, Al-Ameen G-Fresh da mawaƙi Hamisu Breaker, bayan samun su da laifin wulaƙanta takardun Naira.

Mai shari’a S.M. Shuaibu ne ya yanke hukunci, inda ya yi musu ɗaurin wata biyar a gidan yari, bayan sun amsa laifin da ake tuhumarsu a gaban kotu.

Sojoji sun ceto yaro da aka sayar shekaru 3 a Filato Tinubu ya yi ta’aziyyar rasuwar Sarkin Gusau

Hukuncin ya biyo bayan tuhumar da Hukumar EFCC ta shigar da su a gaban kotu, bisa laifin wulaƙanta Naira.

A cewar ƙarar, G-Fresh ya watsa kuma ya taka takardun Naira 1,000 har na Naira 14,000 yayin da yake rawa a shagon wata mai suna Rahma Sa’idu a Ƙaramar Hukumar Tarauni.

Shi kuma Hamisu Breaker, ya watsa Naira 30,000 na takardun Naira 200 a wani taron walima da aka yi a Hadeja da ke Jihar Jigawa.

Dukkaninsu sun aikata laifin ne a watan Nuwamban 2024.

Laifin ya ci karo da Sashe na 21(1) na dokar Babban Bankin Najeriya (CBN) ta shekarar 2007, wadda ta haramta cin zarafi ko wulaƙanta Naira.

Bayan amsa laifinsu, kotun ta ba su damar biyan tara maimakon zaman gidan yari.

Kowannensu ya biya tarar Naira 200,000, wanda hakan ya sa aka sake su bayan tsare su.

Wannan hukunci na nuna cewa gwamnati na ɗaukar wulaƙanta Naira a matsayin babban laifi, duk da cewar akwai damar samun beli ko biyan tara.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Mawaƙi Wulakanta Naira wulaƙanta Naira

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya ta ce Najeriya na rasa sama da Dala Biliyan 10 duk shekara sakamakon asarar amfanin gona bayan girbi.

Ministan Noma  Sanata Abubakar Kyari ne ya bayyana haka a wajen kaddamar da shirin Hanyar Inganta Noma da Kayayyakin Mire Rayuwa a Yankunan Karkara G.R.A.I.N a ƙaramar hukumar Birnin Kudu ta  Jihar Jigawa.

 

Ya ce asarar na faruwa ne saboda rashin ingantattun wuraren ajiya, karancin ababen more rayuwa, sauyin yanayi da kuma ambaliya.

Kyari ya bayyana cewa noma na bada gudunmawar kashi 24 bisa 100 na Jimillar Darajar Kayayyaki da Ayyuka da Kasa ta Samar a Cikin Shekara GDP, inda ƙananan manoma ke samar da sama da kashi 70 bisa 100 na abincin da ake ci a ƙasa.

Ya jaddada cewa gwamnati za ta tallafa musu da kayan noma na  zamani da wuraran kasuwanci domin inganta tattalin arziki.

A nasa jawabin, Gwamna Umar Namadi na Jigawa ya yaba da samun Cibiyar Cigaban Karakara ta Pulse ta farko a Jigawa, yana mai cewa za ta kawo sauyi a harkar noma da rayuwar jama’ar karkara.

Haka zalika, shi ma Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya ce haɗin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu zai taimaka wajen ci gaban tattalin arziki.

Shugaban ƙaramar hukumar Birnin Kudu, Alhaji Builder Muhammad Uba, ya jaddada goyon bayansa ga shirin Renewed Hope Agenda na Shugaba Tinubu tare da yabawa gwamnatin Namadi kan sauya fasalin noma a jihar.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
  • Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • Ƴan Bindiga Sun Sace Malamin Krista Na Ɗarikar Katolika A Kogi