HausaTv:
2025-07-26@09:44:12 GMT

Iran Ta Cilla Tauraron Dan’adam Mai Suna Nahid-2 A Yau

Published: 25th, July 2025 GMT

JMI ta cilla taurarun dan’adam masu suna Nahid-2 kirar cikin gida zuwa sararin samaniya tare da nasara. Kuma ta yi amfani da kombo na kasar Rasha mai suna Vostochiny Cosmodrome don isar da tauraron zawa inda take so a sararin samaniya, a yau Jumma’a 25 ga watan Yulin shekara ta 2025.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta kara da cewa kombon kasar Rasha a wannan cillawar ta isar da taurarin dan’adam da dama zuwa sararin samaniya.

Banda tauraron dan’adam na kasar Iran ita ma kasar Rasha tana da taurarin dana dam guda biyu a cikin kumbon wato Ionosfera-M3 da M4, sannan da wasu 18 na wasu kasashe.

Kafin haka dai wannan kumbon na kasar Rasha ya taba aika taurarin dan’adam na kasar Iran guda 3 wato Khayyam, Parsa -1 da kuma hudhod.

Manufar cilla Nahid -2 dai shi ne kyautata harkokin sadarwa na JMI a sararin samaniya. Kuma kamfanonin gina taurarin yan adama a cikin kasa ne suka hada kai don ganin ya kammala.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: a sararin samaniya kasar Rasha

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jaddada Aniyar Iran Ta Ci Gaba Da Inganta Sinadarin Uranium

Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Babu shakka Iran za ta ci gaba da inganta sinadarn Uranium

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana a jiya Alhamis dangane da tattaunawar da Iran za ta yi da kungiyar kasashen Turai da za a yi a yau Juma’a a birnin Istanbul na Turkiyya cewa; Za a ci gaba da inganta sinadarin Uranium a cikin kasar Iran, kuma kasar ba za ta yi watsi da wannan hakkin na al’ummar Iran ba.

A cikin bayanin da ya yi a gefen ziyarar da ya kai ga iyalan shahidan Laftanar Janar Baqiri, Araqchi ya kara da cewa; Ko da yaushe Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye take ta ci gaba da shirinta na makamashin nukiliya na zaman lafiya bisa tsari mai ma’ana da inganci.

Ya kara da cewa: Iran ba ta taba yin kasa a gwiwa ba wajen samun amincewar kasashe da a wasu lokutan suke nuna damuwa, a maimakon haka, Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta gabatar da bukatunta na mutunta hakkinta na amfani da makamashin nukiliya cikin lumana, ciki har da inganta harkokin makamashi.

Ya ci gaba da cewa: Tattaunawar da za a yi a gobe ci gaba ce ta wadancan shawarwarin da suka gabata, matsayar Iran a bayyane take, wajibi ne duniya ta san cewa ba a samu wani sauyi a matsayin kasar ba, kuma za ta himmatu wajen kare hakkin al’ummar Iran a fagen samar da makamashin nukiliya ta hanyar lumana, musamman batun inganta makamashin nukiliya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Ukraine Ya Nuna Sha’awar Ganawa Da Shugaban Kasar Rasha
  • Iran Da Eu Sun Fara Tattaunawa A Istambul
  • An kai hari a ƙauyuka uku da kashe mutum 7 a Imo
  • Iran Ta Jaddada Wajabcin Daukan Matakin Kawo Karshen Dakatar Da Laifukan Kisan Kare Dangi A Gaza
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jaddada Aniyar Iran Ta Ci Gaba Da Inganta Sinadarin Uranium
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: Taro Tsakanin Iran Da Tawagar Kasashen Turai Dama Ce Ta Gyarar Tunanin Tarai
  • Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar
  • Ayatullahi Makarem Shirazi Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Hadin kai Da Suka Bayar Lokacin Yakin Kwanaki 12
  • A Kalla Falasdinawa 10 Yunwa Ta Kashe A Gaza A Cikin Sa’o’i 24