Aminiya:
2025-07-27@10:25:34 GMT

Za mu ba da damar shigar da kayan agaji a Gaza — Isra’ila

Published: 27th, July 2025 GMT

Isra’ila ta ce za ta bai wa ayarin Majalisar Dinkin Duniya damar shiga Gaza domin raba kayan agaji da magani, bayan makonni na matsin lamba daga hukumomi da kasashen duniya.

Sanarwar da rundunar sojin Isra’ila ta fitar ranar Asabar, ta ce ta bayar damar komawa jefa kayan agajin ta jiragen sama – abin da aka ce bai wadatar ba, baya ga hadarin da ke tattare da shi.

Super Falcons ta lashe gasar WAFCON karo na 10 bayan doke Maroko ADC ce kaɗai za ta iya magance matsalolin Arewa — David Mark

Rundunar sojin ta ce ta fara aiwatar da wasu jerin matakai na inganta kai agajin a yankunan da ke da tarin jama’a

Hakan dai na zuwa ne a yayin da Isra’ilar ke sci gaba da fuskantar matsin lamba daga hukumomi da kasashen duniya da ke bayyana damuwa kan al’ummar Falasdinawa a Zirin Gaza za su fada cikin mummunan bala’in yunwa.

A bayan nan dai Isra’ila ta takaita shigar da kayan agajin da magunguna tsawon watanni ga al’ummar yankin su miliyan biyu, a yayin da take ci gaba da musanta abin da ta kira ikirarin haddasa yunwa ga al’ummar ta Gaza da gangan.

Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito kafofin Falasdinawa suna tabbatar da ci gaba da aikin jefa kayan agajin ta sama, a yankin arewacin Gaza.

Tun daga farkon watan Maris ne Isra’ila ta dakatar da bayar da dukkanin kayan agajin, amma ta bayar da damar bayarwa amma da sababbin sharuda a watan Mayu.

Isra’ila na ci gaba da luguden wuta a Gaza

Aƙalla mutane 25 ne suka mutu a wasu hare-hare ta sama da kuma ta ƙasa da sojojin Isra’ila suka kai cikin dare a yankin Gaza.

Jami’an kiwon lafiya a asibitin Shifa da aka kai gawarwakin mutanen, sun ce mafi yawancinsu an kashe sune ta hanyar harbi da bindiga, a lokacin da suke dakon isowar motocin kayan agaji ta mashigar Zikim.

Wannan dai na zuwa ne dai-dai lokacin da tattaunawar da ake yi don cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Hamas ta fuskanci koma baya, sakamakon yadda Amurka da Isra’ila suka janye wakilansu a ranar Alhamis.

A ranar Juma’a ce firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, ya ce gwamnatinsa na duba yuwuwar cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakaninsu da Hamas, kalaman da ke zuwa dai-dai lokacin da jami’in Hamas ke cewa ana saran a mako mai zuwa ne za su ci gaba da tattaunawa kan batun.

Ƙasashen Masar da Qatar waɗanda ke shiga tsakani a tattaunawar tare da Amurka, sun ce an dakatar da tattaunawar ce na ɗan ƙaramin lokaci, kuma za a ci gaba da ita duk da yake ba su bayyana zuwa wane lokaci ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Benjamin Netanyahu Isra ila yunwa kayan agajin Isra ila ta

এছাড়াও পড়ুন:

 Gaza: Ana Ci Gaba Da Samun Shahidai Da Yunwa Take Kashewa A Gaza

A daidai lokacin da aka cika kwanaki 659 daga fara kisan kiyashin Gaza, sojojin Sahayoniya suna ci gaba da killace yankin da hana shigar da abinci da magani.

Ma’aiktar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa ya zuwa wannan lokacin jumillar wadanda yunwa ta kashe sun kai 122 daga cikinsu da akwai kananan yara 83.

Da jijjifin safiyar yau Asabar, majiyar asibitin “Nasr’ ta sanar da cewa wata jaririya ta yi shahada saboda rashin abinci mai gina jiki. Haka nan kuma ta ce, jaririyar ‘yar watanni 6 da haihuwa ta yi shahada ne saboda rashin abinci mai gina jiki da kuma magani saboda takunkumin da HKI ta kakabawa yankin na Gaza.

Babban jami’iin gudanarwa na ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza Dr. Munir al-Bursh ya sanar da cewa; Ana kara samun masu mutuwa saboda yunwa, musamman ma dai a tsakanin kananan yara.

Al-Bursh ya fada wa tashar talabijin din al-jazira cewa; Yunwa saboda rashin abinci da kuma rashin Magani ya sa jariran da suke cikin  mata 3,000 sun mutu.

Haka nan kuma ya nuna mamakinsa akan yadda duniya ta gajiya wajen iya shigar da madarar jarirai cikin yankin Gaza domin ceto da rayuwar kananan yara da jarirai.

A wannan tsakanin ne dai Asusun kananan yara na MDD ( Unicef) ya yi gargadi akan mummunan halin da yaran Gaza suke ci gaba da shiga saboda rashin abinci mai gina jiki.

Ita kuwa shugabar hukumar Agaji ta kasa da kasa “Rd Cross” ta yi kira ne da a kawo karshen wahalhalu da bala’in da aka jefa mutane a Gaza, cikin gaggawa ba tare da ba ta lokaci ba.

A wani labarin na daban, kafafen watsa labarun HKI sun ce, sojojin Sahayoniya sun lalata tarin abinci mai yawa da aka ware domin shigar da shi zuwa yankin Gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Furuci Da Halakar Sojan Guda Da Ya Jikkata A Zirin Gaza
  • Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza
  • Tallafin Lafiya: Ƙungiyar Rotary Ta Raba Kayan Haihuwa kyauta Ga Mata Masu Juna Biyu  A Kaduna
  •  Gaza: Ana Ci Gaba Da Samun Shahidai Da Yunwa Take Kashewa A Gaza
  • ‘Yan Jarida Da Suka yi Shahada A Gaza Sun Kai 232, Yayin Da Wadanda Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Yunwa Suka Kai 122
  • Hukumar Ba Da Agajin Jin Kai Ta ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinawa Ta “UNRWA” Ta Sanar Da Kashe Ma’aikatan 330 A Gaza
  • Iran da Bangladesh sun bukaci taron gaggawa na OIC kan kisan kiyashi a Gaza
  • Fiye Da  Falasdinawa 111 Ne Su Ka Yi Shahada Saboda Yunwa A Gaza
  • Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Fara Tattaunawa kan Masifar Zirin Gaza Na Falasdinu