Za mu ba da damar shigar da kayan agaji a Gaza — Isra’ila
Published: 27th, July 2025 GMT
Isra’ila ta ce za ta bai wa ayarin Majalisar Dinkin Duniya damar shiga Gaza domin raba kayan agaji da magani, bayan makonni na matsin lamba daga hukumomi da kasashen duniya.
Sanarwar da rundunar sojin Isra’ila ta fitar ranar Asabar, ta ce ta bayar damar komawa jefa kayan agajin ta jiragen sama – abin da aka ce bai wadatar ba, baya ga hadarin da ke tattare da shi.
Rundunar sojin ta ce ta fara aiwatar da wasu jerin matakai na inganta kai agajin a yankunan da ke da tarin jama’a
Hakan dai na zuwa ne a yayin da Isra’ilar ke sci gaba da fuskantar matsin lamba daga hukumomi da kasashen duniya da ke bayyana damuwa kan al’ummar Falasdinawa a Zirin Gaza za su fada cikin mummunan bala’in yunwa.
A bayan nan dai Isra’ila ta takaita shigar da kayan agajin da magunguna tsawon watanni ga al’ummar yankin su miliyan biyu, a yayin da take ci gaba da musanta abin da ta kira ikirarin haddasa yunwa ga al’ummar ta Gaza da gangan.
Kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito kafofin Falasdinawa suna tabbatar da ci gaba da aikin jefa kayan agajin ta sama, a yankin arewacin Gaza.
Tun daga farkon watan Maris ne Isra’ila ta dakatar da bayar da dukkanin kayan agajin, amma ta bayar da damar bayarwa amma da sababbin sharuda a watan Mayu.
Isra’ila na ci gaba da luguden wuta a GazaAƙalla mutane 25 ne suka mutu a wasu hare-hare ta sama da kuma ta ƙasa da sojojin Isra’ila suka kai cikin dare a yankin Gaza.
Jami’an kiwon lafiya a asibitin Shifa da aka kai gawarwakin mutanen, sun ce mafi yawancinsu an kashe sune ta hanyar harbi da bindiga, a lokacin da suke dakon isowar motocin kayan agaji ta mashigar Zikim.
Wannan dai na zuwa ne dai-dai lokacin da tattaunawar da ake yi don cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Isra’ila da Hamas ta fuskanci koma baya, sakamakon yadda Amurka da Isra’ila suka janye wakilansu a ranar Alhamis.
A ranar Juma’a ce firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, ya ce gwamnatinsa na duba yuwuwar cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakaninsu da Hamas, kalaman da ke zuwa dai-dai lokacin da jami’in Hamas ke cewa ana saran a mako mai zuwa ne za su ci gaba da tattaunawa kan batun.
Ƙasashen Masar da Qatar waɗanda ke shiga tsakani a tattaunawar tare da Amurka, sun ce an dakatar da tattaunawar ce na ɗan ƙaramin lokaci, kuma za a ci gaba da ita duk da yake ba su bayyana zuwa wane lokaci ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Benjamin Netanyahu Isra ila yunwa kayan agajin Isra ila ta
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
Kwamitin bincike mai zaman kansa na Majalisar Dinkin Duniya, ya fitar da wani rahoto mai zargin Isra’ila da laifin aikata kisan kiyashi a zirin Gaza.
A cikin sabon rahoto da ta gabatar a ranar Talata, MDD ta zargi shugaban kasar Isra’ila Isaac Herzog, da firaministan kasar Benjamin Netanyahu, da kuma tsohon ministan tsaro Yoav Gallant da “kimsa kisan kiyashi.”.
Rahoton ya tattara batutuwan da suka shafi farar hula kai tsaye, ciki har da yara, ya kuma bayyana cewa kisan kiyashin da ake yi ya fi yawa fiye da yadda aka yi tashe-tashen hankula a baya.
Masu binciken sun kuma tabbatar da cewa da gangan Isra’ila ta haifar da yanayin da ke barazana ga rayuwar Falasdinawa ta hanyar toshe hanyoyin samun muhimman kayayyaki na wannan al’umma.
Rahoton ya biyo bayan wani bincike da aka yi na tsawon shekaru biyu, kuma ya yi nuni da yadda ayyukan Isra’ila ke a matsayin kisan kare dangi.
A martanin da ta mayar, Isra’ila ta yi watsi da sakamakon binciken da cewa “karya ce “, ta kuma bukaci da a rusa hukumar nan take.
A sa’i daya kuma, kwamitin bincike na MDD ya yi kira ga kasashe da su daina baiwa Isra’ila makamai da kayan aikin da za a iya amfani da su wajen aikata kisan kare dangi.
Fitar da rahoton na zuwa ne mako guda gabanin babban taron Majalisar Dinkin Duniya a birnin New York, inda ake sa ran kasashe da dama za su amince da kasar Falasdinu a hukumance.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran da Saudiyya sun bukaci hadin Musulmi game da halin da ake ci a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Tashar Jirgin Ruwan Hudaida Dake Yamen September 16, 2025 Iran Ta Gabatar Da Sabbin Kayayyaki 5 A Wajen Taron kere-kere . September 16, 2025 Iran Ta Bukaci IAEA Tayi Tir Da Harin Da Isra’ila Ta Kai A Tashoshin Nukiyarta. September 16, 2025 Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana September 16, 2025 Pezeshkian: Saudiyya Na Iya Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Samar Da Hadin Kan Kasashen Musulmi September 16, 2025 Pezeshkian: Ta’addancin Haramtacciyar Kasar Isra’ila Kan Kasar Qatar Zalunci Ne Ga Diflomasiyya September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci