An Fara Zaman Jin Ra’ayoyin Jama’a Kan Sauya Kundin Tsarin Mulki A Kano
Published: 27th, July 2025 GMT
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibril, ya kaddamar da zaman jin ra’ayoyin jama’a na yankin Arewa maso Yamma kan sauya kundin tsarin mulkin Najeriya a Kano.
Yayin gabatar da jawabinsa na bude taron, Sanata Barau ya yi maraba da manyan baki da suka halarci zaman, yana mai cewa: “Ina alfahari da zuwanku wannan zama na jin ra’ayoyin jama’a na yankin Arewa maso Yamma, wanda ya shafi kudurori da sabbin batutuwa dangane da gyaran kundin tsarin mulkin Tarayyar Najeriya.
Sanata Barau ya tunatar da cewa Majalisar Ƙasa ta riga ta amince da gyaran kundin tsarin mulki sau biyar, da aka fi sani da alteration acts na farko zuwa na biyar.
Ya jaddada cewa akwai muhimman batutuwa da ke buƙatar ƙarin matakin doka domin warware su. Cikin batutuwan da za a mayar da hankali a kansu akwai: Sauye-sauyen harkar zaɓe, gyara a fannin shari’a, gyaran kundin tsarin mulki, da gudanar da shari’u da tsare-tsarensu.
Sauran muhimman batutuwa sun haɗa da:Inganta ‘yancin ɗan adam, tabbatar da shigar mata a harkokin shugabanci, raba iko da haɓaka ci gaban ƙananan hukumomi, batutuwan tsaro da tsarin aikin ‘yan sanda, da sauransu.
Sanata Barau ya buƙaci dukkan masu ruwa da tsaki da su ba da ra’ayoyi da shawarwari, yana mai cewa: “Mun buɗe ƙofofinmu ga dukkan ra’ayoyi. Kwamitin ya kuduri aniyar sauraron dukkanin bangarori yadda yakamata.” In ji shi.
Ya jaddada cewa shiga cikin irin wannan tsari na jama’a muhimmin al’amari ne ga makomar ƙasa.
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, wanda Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jiha, Dr. Wali Sani, ya wakilta, ya jaddada bukatar haɗin kai, adalci da daidaito. A cewarsa: “ya zama mu yi ayyukan da za su haɗa ƙasa, su inganta adalci da daidaito, su kuma haɓaka ci gaba da bunƙasa tattalin arzikin ƙasa gaba ɗaya.”
Abdullahi Jalaluddeen
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: kundin tsarin Sanata Barau
এছাড়াও পড়ুন:
Daruruwan Jama’a Sun Halarci Sallar Jana’izar Marigayi Sarkin Gusau
Daruruwan mutane daga sassa daban-daban na Jihar Zamfara da wajen ta sun halarci Sallar jana’izar marigayi Sarkin Gusau, Dr. Ibrahim Bello, wanda ya rasu a daren Alhamis bayan gajeruwar rashin lafiya.
An gudanar da Sallar jana’izar ne a Masallacin Jumu’a na Gusau da ke Kanwuri, inda Mataimakin Babban Limamin masallacin, Malam Abdulkareem Umar, ya jagoranci addu’o’in.
172-days_english-3316981
Daga cikin manyan baki da suka halarta har da Gwamnan Jihar Zamfara, Dr. Dauda Lawal, wanda ya bayyana marigayin a matsayin Uba ga kowa, shugaba mai son zaman lafiya, kuma mutum mai hikima wanda ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen ci gaba da hadin kan jihar.
Gwamna Lawal ya nuna alhini matuka game da rasuwar Sarkin, inda ya yi addu’ar Allah ya jikansa ya gafarta masa. Ya kuma bukaci al’ummar jihar da su yi koyi da kyawawan halayen marigayin na tawali’u, adalci da kokarin tabbatar da zaman lafiya.
Haka zalika, mataimakin gwamna, Mani Malam Mummuni, sakataren gwamnatin jihar, manyan jami’an gwamnati, ‘yan majalisar dokoki ta jiha, sarakuna, malamai da daruruwan al’ummar gari daga fannoni daban-daban sun halarci Sallar.
Su ma ‘yan majalisar wakilai da ke wakiltar Maru/Bungudu da kuma Gusau a Majalisar Wakilai ta Tarayya, Dr. Abdulmalik Zannan Bungudu da Kabiru Ahmad Maipalace, sun halarci jana’izar.
Haka kuma dukka sarakunan masu daraja ta farko a Jihar Zamfara da hakimai daban-daban sun halarci sallar jana’izar.
Marigayi Sarkin Gusau, Dr. Ibrahim Bello, wanda ya hau karagar mulki a shekarar 2004, ya shahara fannin ilimi, da kuma kokarin tabbatar da zaman lafiya a Jihar Zamfara.
Rasuwarsa ta zamto babban rashi ga masarautar da ma al’ummar jihar baki ɗaya.
An binne shi a makabartar Kwata da ke Gusau, yayin da ake ci gaba da zuwa ta’aziyya da yi masa addu’a.
Daga Aminu Dalhatu