Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja
Published: 24th, July 2025 GMT
An samu ɓarkewar cutar amai da gudawa wato kwalara a ƙananan hukumomi shida na Jihar Neja, inda rahotanni suka ce mutum 13 ne suka mutu tare da wasu mutane sama da 236 da ke jinya a asibiti.
An fara samun ɓullar cutar ne a Ƙaramar hukumar Shiroro tun a ranar Lahadin da ta gabata zuwa Ƙananan hukumomin Bosso da Minna da Magama da Bida da Munya, inda jami’an kiwon lafiya suka tabbatar da ƙaruwar ɓullar cutar a ƙananan hukumomin da abin ya shafa.
Majiyoyi sun bayyana cewa, yankunan Chanchaga a Minna da Bosso da Shiroro na daga cikin yankunan da lamarin ya fi ƙamari, lamarin da ya sa gwamnatin jihar ta ɗauki matakin gaggawa na kiwon lafiya.
Kwamishinan lafiya a matakin farko, Dakta Ibrahim Dangana, ya tabbatar da ɓullar cutar, ya kuma ce jihar ta ɗauki matakai da dama domin daƙile yaɗuwar cutar.
A cewarsa, an kafa cibiyoyin kula da lafiya da killace marasa lafiyan a kowace ƙaramar hukumar da abin ya shafa.
Dangana ya ce “Mun kafa cibiyoyin kulawa da killace masu jinya don rage yaɗuwar cutar, kuma muna kuma wayar da kan jama’a kan cutar,” in ji Dangana.
Ya ƙara da cewa, “Shirin wayar da kan jama’a ya shafi Ƙungiyoyin addini irin su Ƙungiyar Kiristoci ta Najeriya (CAN), kungiyoyin Islama, da masarautu takwas da ke jihar”.
Domin ƙarfafa ƙoƙarin hana yaɗuwar cutar, gwamnatin jihar ta buɗe cibiyar killacewa a tsohon reshen cibiyar kula da lafiya na matakin farko na Marigayi Sanata Idris Ibrahim Kuta daura da tsohon titin filin jirgin sama a Minna.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kwalara
এছাড়াও পড়ুন:
Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
Gwamnatin Jihar Jigawa ta amince da ƙarin kasafin kuɗi na Naira Biliyan 75 na shekarar 2025, ga gwamnatin jiha da kuma ƙananan hukumomi 27.
Kwamishinan Yaɗa Labarai, Matasa, Wasanni da Al’adu na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ne ya bayyana haka jim kaɗan bayan zaman majalisar da aka gudanar a gidan gwamnati dake Dutse, babban birnin jihar.
Ya bayyana cewa, wannan ƙarin kasafin kuɗi ya samo asali ne daga ƙarin kuɗaɗen shiga domin biyan buƙatun kuɗaɗen da suka taso, da kuma ƙarfafa manyan fannoni da za su kawo ci gaba mai ɗorewa a faɗin jihar.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya ce, majalisar ta amince da Naira Biliyan 58 ga gwamnatin jiha da kuma Naira Biliyan 17 ga Kananan Hukumomi 27, wanda ya shafi kashe-kashen kudade na yau da kullum da kuma manyan ayyuka.
Ya ce, wannan ƙarin kasafin kuɗin zai inganta ayyuka da tsare-tsare da ake gudanarwa a muhimman fannoni irin su ilimi, kiwon lafiya, ababen more rayuwa, noma da sauran muhimman ayyukan ci gaba.
Sagir ya ƙara da cewa, za a mika ƙarin kasafin kuɗin ga Majalisar Dokokin Jihar domin tattaunawa da amincewa da shi, kamar yadda kundin tsarin mulki da ka’idojin kasafi suka tanada.
Kwamishinan ya ƙara jaddada cewa, wannan mataki ya nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen gudanar da mulki bisa gaskiya da adalci, da kula da kuɗaɗen jama’a yadda ya dace, da kuma tabbatar da samar da ingantattun ayyuka ga al’ummar jihar baki ɗaya.
Usman Muhammad Zaria