Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa
Published: 26th, July 2025 GMT
Sunana Yasar Sale Zareku Miga A Jihar Jigawa:
Gaskiya aurar da yarinya ga mutum mai shekaru ya fi, dan shi zai fi kula da hakkinta ya san rayuwa, ni ban ga wata matsala ba dan mace ta auri mutum mai shekaru. Shawarata shi ne iyaye su san wanda ya kamata su aurawa ‘ya’yansu, domin aure muhimmin al’amari ne da ya kamata a zurfafa bincike kafin a gudanar, domin gudun yin kitso da kwarkwata daga karshe nake addu’ar Allah ya bawa mata miji nagari su ma mazan Allah ya ba su mata nagari.
Sunana Rahama Bashir daga Jihar Katsina:
Ni a gani na auren namijin da ya girmeka ya fi musamman idan shekarun da yawa, sabida kar ku tsufa tare, amma idan namiji shekararku tazarar ba yawa za ku tsufa tare karshe ya fara ganin kin yi masa tsufa bari ya nemo karamar yarinya, amma idan ya baki shekaru da yawa kamar goma ko goma sha ko ashirin to, zai ta ganinki a yarinya komai ki ka yi kuruciya ne sabida ya wuce wajen ke kuma yanzu ki ke zuwa, tunanin ma ya auro yarinya ba zai yi ba tunda bai gama da naki kuruciyar ba.
Sunana Ibrahim Garba Bizi Daga Damaturu, Jihar Yobe:
Wannan batu shi yafi dacewa a yi mata aure da wanda ya fita shekaru, ba rashin amfani sai dai amfano, in ta auri sa’anta ko wanda ya fita da shekara 1 ko 2 za ta tsufa ta bar shi, amma in ta auri wanda ya fita shi ne wanda tafiyar za ta wanye lafiya. Ba wata masala da za ta haifar face ta haifar da maslaha. Su daure su cije su bawa wanda suka ga ya cancanta ba sai mai dukiya ba ko mai azuki ba, yawanci ana ba masu manyan shekaru yara kananu saboda arzikinsu.
Sunana Aisha T. Bello daga Jihar Kaduna:
Wasu iyayen kwadayi ne ke kai wa da haka kuma irin haka na jawo matsala irin-irin mussaman ga yarinya karama cutarwa ce babba, wata daga gun haihuwa ake samun matsala. Gaskiya nafi ganin kwadayi ne kawai, saboda da tsoho ya zo neman aure in yana da kudi kawai sai a bashi saboda na ga irin wannan da yawa gaskiya. Eh to matsala in yana da yara manya to za ka ga abubuwa irin gaskiya sai dai ki ta hakuri. Shawara ta a nan ita ce kowace mata a duniya Allah ya tsara mata rayuwar ta na daniya to, dan Allah iyaye mu bi zabin Allah shi ne mafita Allah ya sa mu dace.
Sunana Muktari Sabo Jahun Jihar Jigawa:
Eh gaskiya yi wa yarinya aure da wanda ya fita shekaru ba wani abu bane matukar dai tana sonsa don hakan ya sha faruwa, kuma ba wata matsala inda matsalar take dai kawai shi ne in ba ta so. Amfanin yi wa yarinya aure da wuri yana da yawa musamman a wannan zamani namu zai taimaka wajen samar wa yarinya da iyayenta kwanciyar hankali. Maganar mijin da ya fi ta shekaru kuwa indai mutumin kirki ne zai kula da hakkinta ai ba matsala bane domin an yi da yawa. Matsala kawai za ta faru ne idan dama dole aka yi mata ko kuma wata bukata aka yi amfani da ita don biyan bukatar. Shawara a nan ita ce iyaye su aurawa ‘ya’yansu mutanen kirki koda kuwa ba masu kudi bane kuma su tabbatar ba su yi musu dole ba.
Sunana Abba Abubakar Yakubu, daga Jos:
Ban ga laifin auren mai shekaru ba.
A ganina babu laifi don karamar yarinya matashiya ta auri wanda ya girme ta, saboda dama bisa dabi’ar halittar mace, ba ta iya zama da wanda suke daidai a shekaru ko kusa da haka. Saboda tana iya fin sa wayo, hikima da dabarar sanin rayuwa. To, shi kuma aure, musamman karkashin koyarwar addini, wanda ya karfafa namiji a kan mace, ana bukatar namijin da zai auri mace, ya kula da rayuwarta, tarbiyyarta da addininta. Duk da kasancewar addini bai hana irin wannan aure da ake samun tazarar shekaru tsakanin miji da mata ba, amma kuma ba uzuri ba ne a aurar da karamar yarinyar da ba ta yi wayo sosai ba, ko kuma jikinta bai rika sosai ba, ga mutumin da yake dattijo mai yawan shekaru ko wanda ba shi da isasshiyar lafiya. Yana da kyau iyaye su rika la’akari da yanayin shekarun yarinya, yanayin cikar halittar ta da kuma wayewarta, kafin su aurar da ita ga wanda zai iya cutar da rayuwarta. Harwayau, kuma ina so in ja hankalin ‘yan mata da su yi la’akari da halayyar wanda suke so, addininsa da sana’arsa ko aikinsa, don ganin ya dace da irin mijin da suke so su aura, ba tare da lura da shekarun sa ba. Matukar mutum yana da halayen kwarai da za ta iya zama da shi a matsayin mijin aure, ina ganin ba sai shekarunta da nasa sun zama daya ba, ko ya zama tazararsu ba ta da yawa ba.
Sunana Comr. Nr. Ibrahim Lawan Stk Sule Tankarkar Jihar Jigawa:
Maganar aure tsakanin yarinya da mutumin da ya manyanta wannan ba wani sabon abu bane ba kuma abu ne da bai sabawa addini ko al’ada ba abin da ya kamata ayi la’akari da shi ko kuma a lura da shi shi ne soyayya da kuma kauna, domin kuwa ni a nawa ganin indai tana son shi shi ma yana sonta wannan ba wani abun damuwa bane kuma hakan zai yi matukar basu dama da kuma lokaci na morewa rayuwar su, haka ma idan aka bar ta ta auri saurayi indai tana son shi shi ma hakan daidai ne. Haka kuma barinta ko bata damar mallakar hankalin shi ma wani abun lura ne, domin kula da lafiyarta da yaran da za ta haifa kawai dai abun da ya kamata mu sani a nan shi ne; kaucewa auren dole da kuma yi mata auren wuri wanda abubuwa ne da ka iya tauye mata hakkinsu ta bangaren cigabansu, iliminsu, lafiyarsu, tunaninsu zamantakewarsu da ma dai abubuwa da dama ta bangarori daban-daban. Sannan ya kamata ake lura da kauna da soyayya tsakanin mace da namiji walau babban mutum ko kuma dai yaro daidai sa’anta wannan shin zai tabbata da zaman lafiya da kuma cigaban zamantakewa a cikin al’umma. Amfanin auren yarinya da kuma namijin da ya fita da wuri na iya sawa yarinyar ta koyi wasu dubarun zama da manyan mutane da kuma yadda za ta kula da su, haka kuma za ta samu kulawa ta musamman da kuma biyawa kanta bukatun rayuwar yau da kullum sai dai rashin amfanin ya fi amfanin da yawa musamman idan ba ta sonsa duk abin da ta samu daga gare shi za ta yi kokarin farantawa wanda take so ne a boye kuma hakan na iya sawa ta fada aikata ba daidai ba da asalin saurayinta da take so, auren namiji da ya girmi yarinya na tauyewa yarinya hakkinta wanda suka hada da hakkin samun nutuwar zaman aure, rashin biyan bukatar sunnar zaman aure a gare shi, wanda ka iya taba lafiyarta, iliminta da tunaninta hadi da cigabanta a rayuwarta na yau da kullum.
Sunana Hassana Yahaya Iyayi (Maman Noor graphics), daga Jihar Kano:
Wani lokaci auren wanda ya mallaki hankalinsa ya fi auren kusan tsarerka shekara daya biyu duk kusan sa’ani ne duk aure na gani inaso kana so ya fi armashi, sannan kowa ya san ciwon kansa. Auren mai shekaru wani lokacin sai ka ga yarinya da kuruciyarta kafin ta gama cin lokacinta mijin ya tsufa sai ka ga ana ‘yan tsale-tsale. Iyaye dai su bari yarinya ta mallaki hankalinta Allah ya kawo wanda za su daidaita. Ba shi da wani amfani in dai yarinya ba tashi tayi da fitina ba bari lokacinta yayi tukun in Allah ya kawo abokin hadin sai ayi. Ana samun matsaloli barkatai daga baya ki ga yarinya ta fandare wata ma dai ki ga tana ‘yan tsale- tsale. Su yi hakuri su bari Allah kawo lokacinsu auren cikin salama kowa na so ya fi ba ruwansu da wata matsala.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
Sojoji biyu sun ji rauni bayan wani harin kwanton baya da ’yan bindiga suka kai kan ayarin motocin Kwamandan kwamandan Rundunar Sojoji ta 382 Ƙaramar Hukumar Faskari ta jihar Katsina.
Lamarin ya faru ne a ƙauyen Ruwan Godiya, kan hanyar Sheme–Kankara, lokacin da tawagar Operation Fansan Yamma (OPFY) ke wucewa.
Ganau sun ce sojojin na kan hanyar ziyartar sansanonin sojoji a yankunan Faskari da Mabai da Ɗan Ali lokacin da aka kai musu hari.
Sai dai sun yi nasarar tunkarar ’yan bindigar har suka kuvuta, kodayake sojoji biyu sun samu raunuka na harbi kuma aka kai su asibitin sojoji domin jinya.
An kai wa sojojin harin ne a rana ɗaya da shugabannin al’ummar Faskari suka zauna da wakilan ’yan bindiga domin rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya.
’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBSHakan ya sanya Faskari zama ƙaramar hukuma ta baya-bayan nan da ta shiga irin wannan sulhu bayan ƙananan hukumomin Ɗanmusa da Jibia, Batsari da Ƙanƙara, Kurfi da Musawa.
Yarjejeniyar na neman kawo ƙarshen tashin-tashina, garkuwa da mutane da kuma ƙaura da ake fama da su a jihar.
Amma akwai shakku kan ɗorewar ta, domin wasu daga cikin shugabannin ’yan bindigar sun bayyana cewa sulhun ya shafi ƙananan hukumomin da suka shiga yarjejeniyar kawai, lamarin da ya janyo tsoron cewa sauran wuraren da ba su rattaba hannu ba, suna iya ci gaba da fuskantar hare-hare.
Wasu mazauna Ruwan Godiya sun ce ayyukan ’yan bindiga na ƙara ta’azzara a sassan Katsina duk da yarjejeniyar sulhun da aka ƙulla da wasu daga cikin shugabanninsu.
Masana sun bayyana cewa hakan ya nuna raunin irin waɗannan tsare-tsare na sulhu, tare da tabbatar da buƙatar ƙarin sa-ido a yankunan da ke fuskantar barazana.
Sulhun Faskari da ’yan bindigaƘaramar Hukumar Faskari ta zama ta baya-bayan nan a Jihar Katsina da ta shiga yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga, domin kawo ƙarshen kashe-kashe, garkuwa da mutane da kuma ƙaura da ake fama da su a yankin.
Kamar sauran sulhunan da aka kulla a ƙananan hukumomi guda shida, sharuddan yarjejeniyar sun ba wa ’yan bindiga damar shiga garuruwa da kasuwanni da asibitoci.
Haka kuma, za su sako duk wanda aka yi garkuwa da shi ba tare da sharaɗin ba. A sakamakon haka, al’umma za su iya komawa gona da kasuwanni cikin kwanciyar hankali ba tare da fargabar farmaki ba.
Yarjejeniyar ta biyo bayan taron al’umma da aka yi a Faskari, inda fitaccen shugaban ’yan bindiga, Ado Aliero, wanda ake nema ruwa a jallo, ya tabbatar wa manoma tsaronsu.
“Daga yau kowa ya koma gona cikin kwanciyar hankali; ba abin da zai faru a Faskari baki ɗaya,” in ji Aliero cikin wani bidiyo da Aminiya ta gani.
Aliero ya ɗora laifin rushewar yarjejeniyar da aka yi a baya kan cafke ɗansa, yana mai cewa ya bi duk hanyoyin lumana, amma abin ya gagara, kafin ya koma tayar da hankali.
A wani bidiyo daban kuma, wani ɗan bindiga da aka gani sanye da rigar harsashi ya zargi hukumomi da nuna wariya da rashin adalci, yana mai cewa sulhu na gaskiya zai tabbata ne kawai idan aka yi adalci ga kowa.
Sai dai duk da rahotannin da ke cewa jami’an gwamnati da na tsaro sun halarci taron, gwamnatin Jihar Katsina ta nesanta kanta daga wannan yarjejeniyar.
Akwai masu kawo cikas — Gwamna RaɗɗaGwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa, ya ce duk da irin ƙalubalen tsaro da ake fuskanta, gwamnatinsa na samun ci-gaba, sai dai akwai masu ƙoƙarin kawo cikas.
Ya bayyana haka ne a wani taron shawarwari da aka gudanar a Katsina ranar Lahadi, wanda ya tattaro manyan masu ruwa da tsaki ciki har da sarakunan gargajiya da shugabannin siyasa da shugabannin tsaro da masana, ’yan kasuwa da shugabannin addini.
Gwamnan ya ce tsaro ne ginshiƙin ajandar ci-gabansa tare da ilimi da noma da kiwon lafiya da kuma tallafa wa ƙanana da matsakaitan ’yan kasuwa.
Ya sanar da cewa gwamnati za ta gina gidaje 152 ga iyalan da aka raba da muhallansu a Jibia, tare da shirya shirin tallafa wa tubabbun ’yan ta’adda da suka domin kada su koma ɓarna.
Haka kuma ya yaba wa jami’an sa-kai da ƙungiyoyin tsaro na gari da suka taimaka wajen dawo da ƙwarin gwiwa a tsakanin jama’a.
Cikin manyan da suka halarci taron akwai tsohon Gwamna Aminu Bello Masari da dattijo Sanata Abu Ibrahim da fitaccen dan kasuwa Alhaji Ɗahiru Mangal da Sarkin Daura Alhaji Faruk Umar Faruk da tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika, Ministan Gidaje Arc. Ahmed Ɗangiwa, da kuma Hadiza Bala Usman mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsare-tsare.
Sauran sun hada da tsohon Daraktan DSS Alhaji Lawal Daura, tsohon Daraktan NIA Ambasada Ahmed Rufai, tsohon Shugaban Kamfanin na NNPC Injiniya Abubakar Yar’adua da Babban Alƙalin jihar Alhaji Musa Ɗanladi, da kuma manyan hafsoshin soja da dama da suka yi ritaya.
Hakazalika, an samu halartar manyan jami’ai, malamai daga jami’o’i da ƙungiyoyin ƙwadago da ƙungiyoyin farar hula da ’yan kasuwa da sauran shugabanni daga sassa daban-daban na jihar.
Gwamna Radda ya jaddada cewa zai ci gaba da karɓar suka da shawarwari daga masu kishin ƙasa, tare da kira ga haɗin kai domin shawo kan matsalolin tsaro da tattalin arziki da jihar ke fama da su.
A nasa vangarenm Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina, Faruk Lawal Joɓe, ya bayyana cewa gwamnatin Raɗɗa ta samar da sama da ayyuka 35,903 a fannoni daban-daban ta karkashin manufar “Gina Makomarka.”
Joɓe ya bayyana ce an samar da ayyukan ne ta hanyar ɗaukar malamai da shugabannin unguwanni da jami’an tsaro na sa da mafarauta da sauransu domin su riƙa taka rawa wajen wanzar da zaman lafiya.
Ya kuma yi ƙarin haske kan aikin Sabunta Birane na Katsina State Urban Renewal da ya lashe Naira biliyan 74.9 wanda ya shafi manyan ayyuka a Daura da Funtua da Katsina.
Ayyukan sun haɗa da gina sabuwar hanyar Eastern Bypass mai tsawon kilomita 24, titi mai hannu biyu a cikin Katsina, gyaran tituna a Daura da Funtua, da kuma kammala wasu muhimman hanyoyin karkara.
A nasa jawabin, Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida, Dakta Nasir Muazu, ya ce gwamnatin Raɗɗa ta ɗauki matakin rashin tattaunawa da ’yan bindiga.
Ya ce abubuwan da ke haifar da ta’addanci sun haɗa da son zuciya da rikice-rikicen albarkatu da sauyin yanayi, da kuma rashin adalci a cikin al’umma.
Ya ƙara da cewa daga 2011 zuwa 2015 matsalar ta tsaya a ƙananan hukumomi biyar, amma ta bazu zuwa 25 a lokacin tsohon Gwamna Aminu Masari bayan shirin afuwa ya faskara.
Kwamishinan ya bayyana cewa hare-haren soji sun lalata maɓoyar ’yan bindiga da dama, sun buɗe manyan hanyoyi, sannan mutum 628 da suka tsira daga hare-hare sun samu kulawar lafiya a bana.
Ya ce yanzu dakarun Community Watch, masu aikin sa-kai da ’yan banga suna mara baya ga jami’an tsaro da ke amfani da jirage marasa matuƙa da makamai da motocin aiki.
Shugaban Ƙungiyar ƙwadago (TUC) na jihar, Muntari Abdu Ruma, ya gargaɗi gwamnati ta yi taka-tsantsan da yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga lura da yarjejeniyar Kankara ta 2016 da ta gagara.
Haka kuma, shugaban ƙungiyoyin farar hula na jihar, Malam Abdulrahman Abdullahi, ya ce akwai buƙatar ƙarin haɗin kai tsakanin jihohin Arewa maso Yamma wajen yaki da ’yan bindiga. Ya yi nuni da cewa ziyarar da dattawan Katsina suka kai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bisa jagorancin Gwamna Raɗɗa ta fara haifar da sakamako mai kyau a Ƙanƙara da Faskari, amma dole a ci gaba da ayyuka cikin tsari.
A nasa ɓangaren, Sanata Ibrahim Tsauri na jam’iyyar adawa PDP, ya ce taron ya fi karkata wajen bayyana nasarorin gwamnati fiye da ba wa mahalarta dama su yi sharhi.
Duk da haka ya ce idan aka ci gaba da irin waɗannan taruka, za su iya kawo sauyi ga jihar bayan shekaru 15 na ƙalubale.
An ce mahalarta taron sun yi alkawarin mara wa gwamnati baya wajen shawo kan matsalar samari, musamman shaye-shaye da sauran laifuka.
Sauran muhimman shawarwarin sun haɗa da haɗe hanyoyin sadarwa a wuri guda da nufin samun nasarar wannan abu da aka sanya a gaba.