An yanke wa mutum 3 hukuncin kisa kan kisan kai a Gombe
Published: 25th, July 2025 GMT
Babbar Kotun Jiha a Gombe mai lamba ta 3 ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga wasu mutum uku bisa laifin haɗa baki da kuma kisan kai.
Alƙalin kotun Mai shari’a Haruna Kereng ne ya jagoranci shari’ar, inda ya ce kotu ta sami Dauda Mohammed Abubakar (wanda aka fi sani da Agenda) da Kabiru Abubakar (Gwarei) da Ibrahim Suleiman da laifi a kan dukkanin tuhume-tuhumen da ake musu dangane da kisan Ibrahim Yahaya a unguwar Herwagana da ke Ƙaramar Hukumar Gombe a ranar 22 ga Afrilu, 2022.
Kotun ta ji cewa, mutanen ukun sun kai wa Ibrahim Yahaya hari ɗauke da makamai masu haɗari kamar: takubba da wuƙa, inda suka kashe shi tare da jikkata wasu mutane biyu, wato Ahmed Abubakar da Muhammad Ahmed Lawan a lokacin harin.
Shari’ar ta fara tun ranar 17 ga watan Nuwamba, 2022, kuma an kammala ta a ranar Laraba, 24 ga Yuli, 2025.
Kereng ya bayyana cewa masu gabatar da ƙara sun gabatar da hujjoji masu ƙarfi da suka tabbatar da laifin da waɗanda ake tuhuma suka aikata, kamar yadda doka ta tanada a sashe na 97 da 221 na dokar laifuka, wanda ta tanadar da hukuncin kisa ga wanda aka same shi da laifin haɗa baki da kuma kisan kai.
Yayin da yake yanke hukunci, Mai sharia Kereng ya ce “Kowannen ku za a rataye shi a wuyansa har sai an tabbatar da mutuwarsa ta hanyar gwajin likita.”
Ya kara da cewa kotu ba ta da ikon rage hukuncin, don haka ba ta saurari roƙon sassauci ba.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Za mu ci gaba da shirye-shiryen babban taronmu — PDP
Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa za ta ci gaba da shirin gudanar da babban taronta wanda za a yi a ranar 15 da 16 ga watan Nuwamba a Ibadan da ke Jihar Oyo.
Tun da farko, Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja, ta hana jam’iyyar gudanar da taron, inda ta ce PDP ta karya dokokinta na cikin gida.
’Yan bindiga sun sace fasinjoji a cikin motocin bas a Kogi Kotu ta dakatar da gudanar da babban taron PDPMai shari’a James Omotosho, wanda ya jagoranci shari’ar, ya umarci Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), da kada ta karɓi ko ta wallafa sakamakon taron har sai PDP ta cika dukkanin sharuɗan da doka ta tanada.
Sai dai a cikin wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar da yammacin ranar Juma’a, kakakinta na ƙasa, Debo Ologunagba, ya ce jam’iyyar ba za ta dakatar da shirin gudanar da taron ba.
Ya bayyana hukuncin kotun a matsayin tauye haƙƙin dimokuraɗiyya a Najeriya.
Ologunagba, ya ce hukuncin ba zai hana PDP ci gaba da shirye-shiryenta na zaɓen sabbin shugabanni da za su jagoranci jam’iyyar na tsawon shekaru huɗu masu zuwa ba.
Ya yi nuni da cewa Kotun Ƙoli ta tabbatar da cewa jam’iyyu na da ’yancin tafiyar da harkokinsu na cikin gida.
“PDP na kira ga mambobinta da shugabanni a faɗin ƙasar nan da su kuma ci gaba da shirye-shiryen babban taron jam’iyyar,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa jam’iyyar mai bin doka ce, kuma ta umarci lauyoyinta da su ɗaukaka ƙara game da hukuncin kotun.