An yanke wa mutum 3 hukuncin kisa kan kisan kai a Gombe
Published: 25th, July 2025 GMT
Babbar Kotun Jiha a Gombe mai lamba ta 3 ta yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ga wasu mutum uku bisa laifin haɗa baki da kuma kisan kai.
Alƙalin kotun Mai shari’a Haruna Kereng ne ya jagoranci shari’ar, inda ya ce kotu ta sami Dauda Mohammed Abubakar (wanda aka fi sani da Agenda) da Kabiru Abubakar (Gwarei) da Ibrahim Suleiman da laifi a kan dukkanin tuhume-tuhumen da ake musu dangane da kisan Ibrahim Yahaya a unguwar Herwagana da ke Ƙaramar Hukumar Gombe a ranar 22 ga Afrilu, 2022.
Kotun ta ji cewa, mutanen ukun sun kai wa Ibrahim Yahaya hari ɗauke da makamai masu haɗari kamar: takubba da wuƙa, inda suka kashe shi tare da jikkata wasu mutane biyu, wato Ahmed Abubakar da Muhammad Ahmed Lawan a lokacin harin.
Shari’ar ta fara tun ranar 17 ga watan Nuwamba, 2022, kuma an kammala ta a ranar Laraba, 24 ga Yuli, 2025.
Kereng ya bayyana cewa masu gabatar da ƙara sun gabatar da hujjoji masu ƙarfi da suka tabbatar da laifin da waɗanda ake tuhuma suka aikata, kamar yadda doka ta tanada a sashe na 97 da 221 na dokar laifuka, wanda ta tanadar da hukuncin kisa ga wanda aka same shi da laifin haɗa baki da kuma kisan kai.
Yayin da yake yanke hukunci, Mai sharia Kereng ya ce “Kowannen ku za a rataye shi a wuyansa har sai an tabbatar da mutuwarsa ta hanyar gwajin likita.”
Ya kara da cewa kotu ba ta da ikon rage hukuncin, don haka ba ta saurari roƙon sassauci ba.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace
Dakarun Sojin Najeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Ƙananan Hukumomin Rijau da Mariga a Jihar Neja.
’Yan ta’addan sun fito ne daga Jihar Zamfara, yayin da suke tafiya a kan babura ɗauke da muggan makamai.
Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan kisan mutum sama da 100 Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na ƙasaSojoji tare da taimakon jiragen yaƙi na sama sun kai farmaki bayan samun bayanan sirri.
Aƙalla ’yan ta’adda 95 aka kashe a yayin artabun.
Sojojin sun kuma lalata babura 18 tare da ƙwato bindigogi kirar AK-47.
Sai dai an yi rashin sa’a soja guda ɗaya ya rasa ransa a yayin fafatawar.
Dakarun sun sake kai wani farmaki na biyu inda suka ƙwato makamai da yawa tare da tarwatsa ’yan ta’addan.
Jama’a daga Warari, Rijau, da wasu ƙauyuka sun yi murnar nasarar sojojin suka samu.
Da yawa daga cikin mazauna yankunan sun tsere daga gidajensu saboda tsoro, amma sun dawo bayan ganin ƙoƙarin da sojoji suka yi.
A wani faifan bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta, an ga yadda jama’a ke taya sojoji murna da godiya.
Wani mazaunin yankin ya tabbatar da cewa farmakin sojojin ya daƙile shirin kai hare-hare da ’yan ta’addan suka yi.
Wani mazaunin yankin shi ma ya ce ’yan ta’addan na shirin kai hari wasu ƙauyuka a Mariga, amma sun gudu bayan farmakin sojoji.
An kama tsohon kansila kan iƙirarin mallakar shanuA gefe guda kuma, jami’an tsaro sun kama tsohon kansilan Rijau, Mamman Wazo, bisa zargin iƙirarin mallakar shanun da aka ƙwato daga hannun ‘yan ta’adda.
Wata ƙungiyar sa-kai ce ta kama shi tare da abokin aikinsa, kuma aka miƙa su ga ’yan sanda.
’Yan sanda sun ce an samu shanun ne daga yankin Rijau bayan wasu hare-hare da aka kai.
Sojoji sun ceto mutum 138 da aka saceA wani samame na daban daban, sojoji sun ceto mutum 138 da aka sace a Jihohin Zamfara, Borno, da Adamawa.
Mafi yawan waɗanda aka ceto mata da ƙananan yara ne.
An kuma kama wasu mutane da ake zargin suna taimaka wa ‘yan ta’adda da kayan aiki.
A Jihohin Borno da Adamawa kuma, sojoji sun kama abubuwan fashewa da sauran makamai yayin da suka daƙile wasu hare-haren ’yan ta’addan.
Rundunar sojin ta ce za ta ci gaba da kasancewa cikin shiri don kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Sojoji sun gode wa al’umma bisa goyon bayan da suke bayarwa, kuma sun buƙaci mutane su ci gaba da bai wa hukumomi bayanai masu amfani.
Sun tabbatar da cewa za su ci gaba da kare ƙasar nan daga barazanar ta’addanci.