HausaTv:
2025-09-17@22:33:07 GMT

Bakaken Fatar Amruka Da Suke Yin Hijira Zuwa Afirka  Suna Karuwa

Published: 27th, July 2025 GMT

Ana samun Karin bakaken fatar Amurka da suke baro kasar suna dawo wa nahiyar Afirka domin samun kyakkyawar rayuwa a cikinta.

Mafi yawancin bakaken fatar suna nuna rashin gamsuwarsu da yanayin tattalin arziki da kuma siyasa na Amukra da su ka taka rawa wajen sa su, daukar matakin komawa Afirka da can ne asalin kakanninsu.

Wani dan kasar Amurka da ya rika yawo a tsakanin kasashe mabanbanta na Afirka a karshe ya tare a kasar Kenya, ya bayyana yadda yake jin ya saje a cikin nahiyar Afirka fiye da a can Amurka.

Auston Holleman wanda ya shahara da wallafa sakwanni a You Tube ya kara da cewa; Dukkanin mutane a Afirka sun yi kama da juna, ba  kamar acikin turai, ko yankin Latin ba. “

Holleman ya kuma bayyana cewa yanayin siyasar Amruka a halin yanzu ya sa kasar tana fada da duk duniya baki daya.

Tun a 2019 ne dai kasar Ghana ta kaddamar da wani shiri na jawo hankalin bakaken fata a ko’ina suke a duniya domin samun wurin zama a cikinta.

A shekarar 2024 Ghana din ta ba da izinin zaman ‘yan kasa ga bakaken fata 524,mafi yawancinsu daga kasar Amurka.

Tun bayan da  kamfanonin bakaken fata  na Amurka irin su  Adilah su ka koma Ghana, an sami karuwar bakaken fatar da suke komawa can.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 
  • Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha
  • Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
  • Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari
  • Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • Jonathan Zai Jagoranci Taron Tattaunawa Kan Dimokuraɗiyya A Ghana
  • NAJERIYA A YAU: Matsayin Doka Kan Hawa Mumbari Ba Tare Da Izinin Gwamnati Ba
  • Ministan Tsaron Kasar venezuela Ya Gargadi Amurka Dangane Da Kokarin Juyin Mulki A Kasar
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Wasu Al’ummomi Suke Kare Kansu Daga Barnar Ambaliyar Ruwa