Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana farin cikinsa bisa nasarar da tawagar ƙwallon ƙafa ta mata ta Nijeriya (Super Falcons) ta samu a gasar cin kofin Afrika na mata (WAFCON) 2025, inda ya ce yana sa ran karɓar kofin daga hannunsu a Abuja.

A cikin wata hira ta bidiyo da aka yi da shugaban ƙasa jim kaɗan bayan wasan, tare da kyaftin din tawagar, Rasheedat Ajibade, da wasu ‘yan wasan da jami’an tawagar, Tinubu ya taya su murna bisa lashe kofin karo na 10.

Ya ce wannan nasara wata hanya ce da ke ɗaukaka darajar Nijeriya a idon duniya.

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata  Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

“Ina alfahari da ku, Nijeriya gaba ɗaya na alfahari da ku. Kun ɗaga martabar ƙasarmu, ku abin koyi ne a zamanin ku. Ina mika godiya ta musamman ga masu horar da tawagar,” in ji Tinubu, a cewar wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ya fitar. Shugaban ya kuma miƙa saƙon ban girma ga Rasheedat Ajibade da ta samu lambar gwarzon ‘yar wasa a gasar.

Yayin da yake zantawa da tawagar, Tinubu ya yi addu’ar dawowar su lafiya zuwa gida, yana cewa: “Ina fatan zaku iso lafiya, Allah ya saka muku da alheri.” A madadin tawagar, Rasheedat ta gode wa shugaban ƙasa bisa amincewa da biyan cikakken alawus na ‘yan wasan, tana mai tabbatar masa da cewa tawagar za ta ba da dukkan ƙoƙarinta wajen kawo kofin WAFCON zuwa Abuja.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala

 

Da yake mayar da martani ga wannan zargin na Amurka, Bwala ya ce gwamnatin Tinubu tana jajircewa wajen kare dukkan ‘yan Nijeriya ba tare da la’akari da addini ba, yana mai cewa Amurka da Nijeriya sun dade suna hadin gwiwa a yaki da ta’addanci.

 

“Shugaba Bola Tinubu da Shugaba Donald Trump suna da kudiri iri ɗaya a yaƙi da ta’addanci da duk wani nau’in ta’addanci a kan bil’adama,” in ji Bwala.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano November 2, 2025 Manyan Labarai Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima November 1, 2025 Manyan Labarai Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala
  • Tinubu zai gana da Trump kan zargin kisan Kiristoci a Nijeriya 
  • Rikicin PDP: Tsagin Wike ya dakatar da Damagum
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
  • An sake kama shi a cikin ’yan fashi kwana 5 da fitowa daga kurkuku