Leadership News Hausa:
2025-11-03@05:07:04 GMT

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

Published: 26th, July 2025 GMT

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

“Dole ne kasar nan ta samar da wata sabuwar hanya, domin samar da Kifin da zai wadace ta, wanda hakan zai kuma taimaka matuka wajen rage dogaro da shigo da Kifin daga kasashen waje da kuma kara habaka fannin” in ji Ministan.

Oyetola ya kara da cewa, gwamnatin tarayya ta himmatu kwarai da gaske wajen bai wa fannin goyon bayan da ya dace, musamman ta hanyar yin amfani da tsarin kimiyyar fasahar zamani da kuma zuba makudan kudade a fannin.

Kazalika, ya jaddada cewa; gwamnatin tarayya za ta kara kaimi wajen ganin ana samar da wadataccen Kifi a kasar, musamman domin rage dogaro a kan wadanda ake shigowa da su daga kasashen ketare, duba da cewa; fannin na bayar da gagarumar gudunmawa wajen kara bunkasa tattalin azikin kasar.

Kungiyoyiyon da suka halarci ganawar sun hada; manya-manyan masu ruwa da tsaki a fannin na kamun Kifi, kungiyar masu kamun Kifi ta kasa (FCFN), kungiyar masu kama dabbobin ruwa (TADAN), kungiyar masu kiwon Tarwada ta kasa (CAFAN) da sauran makamantansu.

Babban mai bai wa ministan shawara a fanin yada labarai, Bolaji Akinola, a cikin sanwar da ya bayar; bayan kammala taron ya bayyana cewa; Oyetola ya shaida wa mahalartan cewa, ma’aikatar na kara yin kokari wajen tallafa wa mata da matasa da suka rungumi sana’ar yin kiwon Kifi a karkashin shirye-shiyen da ma’aikatar ta kirkiro.

A cewar ministan, wannan shiri ne na tallafa wa mata da matasa; wanda kuma ya hada da tallafa musu da rance da kayan aiki, musaman don kara musu kwarin gwiwa, domin bayar da tasu gudunmawar wajen kara bunkasa fannin a Nijeriya, wanda kuma ya yi daidai na shirin Shugaban Kasa Bola Tinubu (Renewed Hope Agenda).

“Kara yawan matasan da za su rungumi sana’ar kiwon Kifi, wani babban maki ne, na kara samar da wadataccen abinci a fadin wannan kasa, wanda hakan zai kuma kasance wani mataki ne na rage marasa yin aiki a kasar” a cewar Oyetola.

“Mun mayar da hankali wajen tabatar da cewa, ba a bar mata da matasan kasar nan a baya ba, musamman don ganin an inganta rayuwarsu”, in ji Ministan.

A wajen ganawar, masu ruwa da tsaki a fannnin; sun kuma bijiro da wasu kalubale da ke ci gaba da ci wa fannin tuwo a kwarya.

A cewarsu, kalubalen sun hada da; yawan kamun Kifayen a Kogi, rashin samun rance, karancin kayan adana Kifin da ake adana Kifin bayan kamo su.

Sauran su ne, tsadar abincin da ake ciyar da su, wadanda ake shigo wa da su daga ketare, matsalar safararsu, karbar haraji barkatai, wanda ke sanyawa matasa ba sa iya shiga cikin sana’ar.

Sai dai, Oyetola ya bai wa masu ruwa da tsakin tabbacin cewa, wadannan kalubale da suka bijro da su, ma’aikatar za ta lalubo da mafita a kansu.

A cewarsa,  a yanzu ana kan tattaunawa da Bankin Duniya, musamman domin a samu rancen kudi don tallafa wa masu kiwon Kifin a kasa tare da kuma samar musu da Inshora.

Ministan ya ci gaba da cewa, wannan zai kara tabbatar da nasarar da aka samu a shirin zamani na kamun dabbobin ruwa a Dam din Oyan da kuma sauran yankunan da ma’aikatar tasa ta yi hadaka da ma’aikatar albarkatun ruwa ta tarayya da sauran hukumomin gwamnatin tarayya.

“Wannan ganawa, ba iya nan za ta tsaya ba; amma tamkar yanzu ne aka fara ta, domin za a ci gaba da tattaunawa kan yadda za a ci gaba da habaka fannin,” in ji shi.

Shi kuwa a nasa jawabin, Wellington Omoragbon, Daraktan kula da kamun Kifi da sauran dabbobin ruwa, ya sanar da muhimmancin bukatar kara karfafa hadaka, domin jawo masu son zuba hannun jari a fannin, musamman domin a kara samar da wadataccen Kifi a fadin kasar baki-daya.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma

Daga Usman Muhammad Zaria

 

Kananan manoma a jihar Jigawa sun yabawa kungiyar Sasakawa Africa dangane da tallafin da take samarwa a fannin inganta noma.

Yayin tattaunawa da wasu daga cikin wadanda suka ci moriyar shirin musamman manoman shinkafa a garin Chandam dake karamar hukumar Birnin Kudu, sun bayyana cewa tallafin Sasakawa ya habaka noman shinkafar su tare da samun karin kudade.

Manoman sun bayyana cewar shirin ya taimaka masu wajen bunkasa harkokin noma tare da tallafawa al’ummomin su.

Daya daga cikin wadanda suka amfana da shirin a yankin Chandam dake karamar hukumar Birnin Kudu, Buhari Nafi’u, yace Sassakawa Africa ta samar masu da tallafin  noma daban daban.

A cewar sa tallafin sun hada da horo wanda ya taimakawa kananan manoma wajen ganin sun kara samun kudade tare da inganta rayuwar maza da mata a yankin.

Yace a wannan shekarar sun noma amfanin gona mai yawa sakamakon horon da suka samu karkashin shirin, inda suka hadu sukayi noman a kungiyance a yankin Birnin Kudu.

Buhari ya kara da cewar, a shekarun baya suna daukan kwanaki casa’in kafin su girbe shinkafa amma zuwan Sassakawa ya sa sun yi noma tare da girbe amfanin gonan su a cikin kwanaki saba’in saboda irin da kungiyar ta basu.

Yace yanzu haka sun fara amfani da shinkafar da suka noma a gidajen su.

Yace an basu takin zamani kyauta tare da sauran kayayyakin feshi.

Ya godewa tallafin na Sassakawa, yana mai cewar zai cigaba da amfani da irin da aka basu tare da koyar da mazauna yankin abubuwan da aka horar da su akai.

Shi ma Malam Rufai Nasiru daga yankin na Chandam  yace sun kara samun ilimi akan sabbin dubarun noma wanda suka samu daga kungiyar ta Sassakawa.

Yace a bana ya noma buhun shinkafa 8 ba kamar a baya ba da yake noma buhu biyar, yana mai cewa shirin yana da inganci kuma zai cigaba da amfani da irin da kungiyar ta basu.

A garin Chuwasu  dake karamar hukumar Taura, Aminu Babanyara ya bayyana cewar sun ci moriyar shirin ta hanyar samun iri masu inganci da takin zamani da kuma horo akan sabbin dubarun noma.

Yace wasu daga cikin abubuwan da suka koya sun hada da amfani da shara wajen yin taki a gida inda suka ce hakan yasa sun samu karin shinkafa da geron da suke nomawa idan aka kwatanta da shekarun baya.

Babanyara, yace sabbin dubarun da suka koya da kuma irin da Sassakawa suka basu, ya basu damar ninka abin da suka saba nomawa a damina sau uku.

Yace da farko suna da shakku akan amfani  da sabbin irin da sabbin dubarun noman, amma kuma bayan sun gwada a shekaru biyu na farko sun ga alfanun hakan wajen bunkasa amfanin gonan da suke nomawa.

Manoman sun kuma yi kira ga kunyiyar ta Sassakawa ta samar masu da injinan casa domin saukaka masu al’amura.

Malama Amina Abdulrahman wacce tayi jawabi a madadin kungiyar mata manoma a Karamar  Hukumar Taura, tace shirin tallafin Sassakawa ya kawo sauyi a rayuwar su musamman a fannin samun kasuwanci da amfanin gonar da ake sarrafawa don yin abinci mai gina jiki na yara.

A cewar ta an horar da su akan yadda za su samar da abinci mai gina jiki a yankuna tare da yadda za su yi aiki a kungiyance don inganta noma.

A don haka, tayi kira ga kungiyar Sassakawa ta samar masu da injinan sarrafa amfanin gona na zamani.

Yankunan da aka ziyarta sun hada da Chandan dake Birnin Kudu da kuma Sabon Gari shi ma a karamar hukumar Birnin Kudu.

Sauran sun hada da Baranda dake Dutse da kuma Chuwasu dake karamar hukumar Taura.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Kisan Kiristoci: Lauyoyi sun nemi Gwamnatin Tarayya ta tattauna da Amurka
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Gwamnatin Yobe ta ƙaddamar da shirin amfani da ma’adanai
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa