Aminiya:
2025-09-17@23:15:36 GMT

Gwamna Bauchi ya sasanta manoma da makiyaya a Darazo

Published: 27th, July 2025 GMT

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya jagoranci zaman sasanci domin kawo zaman lafiya tsakanin Fulani makiyaya da manoma a garin Nahuta da ke Ƙaramar Hukumar Darazo.

Wannan sasanci na zuwa ne bayan makonni uku da aka shafe ana rashin jituwa tsakanin ɓangarorin biyu.

Ambaliya ta yi ajalin mutane, ta lalata gidaje a Adamawa LP za ta ceto Nijeriya daga halin da APC ta jefa ta — Nenadi Usman

A taron da aka yi a ranar Lahadi, gwamnan ya yaba da yadda dukkanin ɓangarorin suka fahimci juna.

Gwamna Bala, ya buƙaci jama’a da su guji duk wani abu da zai tayar da hankali, tare da yin kira a bin doka da oda.

Ya ce gwamnati tana ɗaukar matakai domin hana rikici tsakanin manoma da makiyaya a jihar.

Taron ya samu halartar wakilan makiyaya da na manoma, ‘yan majalisa, shugabannin ƙananan hukumomi da na al’umma, ciki har da ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Darazo da Ganjuwa.

A yayin taron, Gwamna Bala, ya sanar da kafa kwamitin bincike don gano dalilan rashin jituwa a tsakanin makiyaya da manoma.

Ya kuma bayyana cewa gwamnati ta ware hekta 2,500 na daji a domin ayyukan noma.

Ya nuna damuwarsa cewa wasu jami’ai da sarakunan gargajiya na raba filaye ba bisa ƙa’ida ba.

Gwamnan, ya gargaɗi manoma da ke karɓar filaye daga gwamnati amma suna bayar da su haya.

Ya ce: “Idan ba za ku yi noma da gonakin da aka ba ku ba, gwamnati za ta karɓe su ta bai wa waɗanda za su yi amfani da su.”

Ya ce gwamnati ba za ta amince da tashin hankali ba, kuma za ta ƙara ƙarfafa sasanci da tsaro domin samar da zaman lafiya.

Shugabannin Fulani, Malam Bala da Ahmadu Laddo, sun koka cewa manoma suna ƙoƙarin ƙwace filayen kiwo, kuma a wasu lokuta ana kai wa matansu hari.

Sun ce sun kai ƙara wajen ‘yan sanda da sarakunan gargajiya, amma babu abin da ya sauya.

Wakilan manoma, Mallam Lawal Babayo da mai unguwa Nadada, sun zargi makiyaya da kai musu hari da hana su noma a gonakin da gwamnati ta ware musu.

Wasu sun ce sun karɓi gonaki haya don noma, amma yanzu sun kasa noma, kuma hakan zai hana su samun amfanin gona.

Sun ƙara da cewa shekarun baya sun samu girbi mai yawa a gonakin da ke Darazo da Sade, amma bana rikici ya hana hakan.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, Sani Omolori, ya ce an tura jami’ai don tabbatar da doka da oda a yankin.

Masu jawabai a wajen taron sun yaba da matakin gwamnan, sun bayyana cewa wannan shiri zai taimaka matuƙa wajen wanzar da zaman lafiya a Jihar Bauchi.

Sun roƙi a ci gaba da haɗa kai da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da nasarar sasancin.

 

Ga hotunan yadda taron ya gudana:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Darazo Gwamna Bala Makiyaya makiyaya da

এছাড়াও পড়ুন:

Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 

Mataimakinsa kan harkokin majalisa Honarabul Attahiru Danmadi ne ya wakilci dan majalisar ya kuma tabbatarwa wadanda lamarin ya shafa kokarinsa kan daukar matakan da suka kamata domin tabbatar da tsaron rayukan su da dawowa da zaman lafiya a yankunan.

 

Garuruwan da ‘yan bindigar suka tarwatsa a gundumar Kuchi sun hada da Fakku, sha’alwashi, tulluwa da Rafin- gora a inda mutane bakwai suka rasa rai. A gundumar Jabo kuwa kauyukan da lamarin ya shafa su ne; Gesolodi, Hilya, Guraye, Guma, Chakai, Modo, Badariya, Tafki, Balera, Gudumawa da Rafin shinka.

 

“Mun girgiza kwarai da wannan halin da kuke ciki. A matsayina na wakilin ku, zan ci-gaba da kokarin da ya kamata a majalisa domin ganin jami’an tsaro sun kawo karshen wannan ta’addancin.”

 

Dan Majalisar ya ce ya gabatar da bukata ga Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa domin tallafawa wadanda lamarin ya shafa kuma zai ci- gaba da bibiya domin ganin tallafin ya samu cikin lokaci.

 

Ya ce yana kokarin ganin rundunar sojoji ta kara tura wadatattun jami’ai tare da tallafa masu domin yakar ‘yan ta’addan da wanzar da zaman lafiya a yankunan.

 

Tallafin kayan abinci na gaggawa da dan majalisar ya bayar sun hada da buhuhuwan masara, gero, garin kwaki da kuma kuli- kuli.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Najeriya Na Asarar Dala Biliyan 10 Bayan Girbi Duk Shekara- Gwamnatin Tarayya
  • Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato 
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja