Aminiya:
2025-11-02@19:08:14 GMT

Gwamna Bauchi ya sasanta manoma da makiyaya a Darazo

Published: 27th, July 2025 GMT

Gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed, ya jagoranci zaman sasanci domin kawo zaman lafiya tsakanin Fulani makiyaya da manoma a garin Nahuta da ke Ƙaramar Hukumar Darazo.

Wannan sasanci na zuwa ne bayan makonni uku da aka shafe ana rashin jituwa tsakanin ɓangarorin biyu.

Ambaliya ta yi ajalin mutane, ta lalata gidaje a Adamawa LP za ta ceto Nijeriya daga halin da APC ta jefa ta — Nenadi Usman

A taron da aka yi a ranar Lahadi, gwamnan ya yaba da yadda dukkanin ɓangarorin suka fahimci juna.

Gwamna Bala, ya buƙaci jama’a da su guji duk wani abu da zai tayar da hankali, tare da yin kira a bin doka da oda.

Ya ce gwamnati tana ɗaukar matakai domin hana rikici tsakanin manoma da makiyaya a jihar.

Taron ya samu halartar wakilan makiyaya da na manoma, ‘yan majalisa, shugabannin ƙananan hukumomi da na al’umma, ciki har da ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Darazo da Ganjuwa.

A yayin taron, Gwamna Bala, ya sanar da kafa kwamitin bincike don gano dalilan rashin jituwa a tsakanin makiyaya da manoma.

Ya kuma bayyana cewa gwamnati ta ware hekta 2,500 na daji a domin ayyukan noma.

Ya nuna damuwarsa cewa wasu jami’ai da sarakunan gargajiya na raba filaye ba bisa ƙa’ida ba.

Gwamnan, ya gargaɗi manoma da ke karɓar filaye daga gwamnati amma suna bayar da su haya.

Ya ce: “Idan ba za ku yi noma da gonakin da aka ba ku ba, gwamnati za ta karɓe su ta bai wa waɗanda za su yi amfani da su.”

Ya ce gwamnati ba za ta amince da tashin hankali ba, kuma za ta ƙara ƙarfafa sasanci da tsaro domin samar da zaman lafiya.

Shugabannin Fulani, Malam Bala da Ahmadu Laddo, sun koka cewa manoma suna ƙoƙarin ƙwace filayen kiwo, kuma a wasu lokuta ana kai wa matansu hari.

Sun ce sun kai ƙara wajen ‘yan sanda da sarakunan gargajiya, amma babu abin da ya sauya.

Wakilan manoma, Mallam Lawal Babayo da mai unguwa Nadada, sun zargi makiyaya da kai musu hari da hana su noma a gonakin da gwamnati ta ware musu.

Wasu sun ce sun karɓi gonaki haya don noma, amma yanzu sun kasa noma, kuma hakan zai hana su samun amfanin gona.

Sun ƙara da cewa shekarun baya sun samu girbi mai yawa a gonakin da ke Darazo da Sade, amma bana rikici ya hana hakan.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, Sani Omolori, ya ce an tura jami’ai don tabbatar da doka da oda a yankin.

Masu jawabai a wajen taron sun yaba da matakin gwamnan, sun bayyana cewa wannan shiri zai taimaka matuƙa wajen wanzar da zaman lafiya a Jihar Bauchi.

Sun roƙi a ci gaba da haɗa kai da masu ruwa da tsaki domin tabbatar da nasarar sasancin.

 

Ga hotunan yadda taron ya gudana:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Darazo Gwamna Bala Makiyaya makiyaya da

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 

A jawabinsa yayin taron, Gwamna Sani ya gabatar da kasida mai taken: “Gina Haɗin Gwiwa Domin Ci Gaban Kowa”, inda ya bayyana yadda Jihar Kaduna ke ci gaba da samun nasara a fannoni da dama kamar gyaran birane, bunƙasa noma, da tsarin tallafiwa jama’a.

 

Gwamnan Ya ce tsarin ci gaban jihar yana dogara ne kan faɗaɗa damar tattalin arziki da kare marasa ƙarfi, da ƙarfafa jama’a su samu nasara a rayuwarsu.

 

Gwamna Uba Sani, ya kuma halarci shirin baje koli na birnin Dubai mai taken : “Sauya Arewa a Nijeriya: Jagoranci, Ƙirƙira, da Tasirin Zamantakewa”, inda nan ma ya jaddada cewa jagoranci mai nagarta da amfani da fasaha a mulki suna da matuƙar muhimmanci wajen buɗe damarmaki ga mutane da birane.

 

A yayin taron, Gwamnan ya gudanar da wata ganawa ta musamman da Marwan Bin Galita, Darakta Janar na birnin Dubai inda suka tattauna batutuwan haɗin gwiwa a fannin kirkirar makamashin sharar gida da kula da sharar gida ta zamani, da kuma tsare-tsaren gine-ginen birane na zamani.

 

A ganawar, duk Bangarorin biyu sun amince da zurfafa haɗin kai a fannin fasaha da musayar ƙwarewa domin tallafawa sauyin jihar Kaduna zuwa tattalin arzikin mai ɗorewa.

 

Gwamna Sani ya bayyana cewa halartar Jihar Kaduna a taron (APCS 2025) na nuna shirin jihar na shiga sahun ƙasashen duniya wajen yin haɗin kai, ƙirƙira, da zama abin koyi a fannin ci gaba mai ɗorewa da ci gaban kowa da kowa a fadin Nijeriya da ma duniya baki ɗaya

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Makarantar Kogi Poly Ta Bankaɗo Masu Ƙirƙirar Takardun Kammala Karatu na Bogi October 31, 2025 Labarai Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede October 31, 2025 Labarai Rundunar Sojin Nijeriya Ta Shirya Wa Janar Musa Faretin Gama Aiki October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani
  • Dalilin Gwamnatin Jihar Kuros Riba Na Raba Wa Manoma Taraktoci
  • Gwamna Uba Sani Ya Bayyana Tsare-tsaren Ci Gaban Kaduna a Taron Duniya a Dubai.
  • Gwamna Namadi Ya Bada Motocin Aiki Goma Ga Rundunar ‘Yan Sanda
  • Gwamna Uba Sani Ya Gabatar Da Kudirorin Raya Jihar Kaduna A Taron Ƙoli Na Biranen Asiya A Dubai 
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Manoma a Jigawa Sun Jinjinwa Kungiyar Sasakawa Africa Bisa Bada Tallafi a Harkar Noma
  • Madagascar Ta Sanar da Kafa Sabuwar Gwamnati Tare da Manyan ‘Yan Adawa
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Daliban Makarantar Kudi Suka Fi Na Gwamnati Kokari