ADC Ga Tinubu: Ina Wutar Lantarki Ta Awa 24 Da Ka Yi Wa ‘Yan Nijeriya Alkawari?
Published: 26th, July 2025 GMT
Ya zargi gwamnatin da cewa ba ta dauki kwararan matakai na kawo babban gyara a fannin wutar lantarki ba, sannan ta gaza wajen nuna wani hobbasa game da lamarin ballantana har kuma ta dauki matakin gaggawa a cikin shekaru biyu da ta kwashe tana mulki.
“Mun wuce rabin lokacin wannan gwamnatin, kuma miliyoyin ‘yan Nijeriya na ci gaba da caji wayoyinsu a tashoshin caji na hannu, suna kashe dubban naira wajen sayen man fetur na janareta domin samun wutar lantarki.
“Ina hasken wutan lantarkin da aka yi wa ‘yan Nijeriya al’kawari? Me ya faru da alkawarinku? Kuma har yaushe ‘yan Nijeriya za su ci gaba da zama cikin duhu?”
Ya sake dawo wa da alkawarin Tinubu a lokacin yakin neman zabe, ya ce, “Mai Girma Shugaban Kasa, ka taba cewa, ‘Idan ban gyara wutar lantarki ba, ka da ku sake zabe na.’ Kuma ‘yan Nijeriya sun ji wannan. Za mu cika maka burinka a 2027.”
Bidiyon kamfen da Abdullahi yake yadawa a kafafen sadarwa na zamani, ya nuna inda Tinubu yake, “Zan bi duk wata hanyar na samur da cikakken wutar lantarki. Kuma ba za ku sake biyan kudin wutan lantarkin da ba ku shafa. Kyan alkawari cika. Idan ban cika alkawarin da na yi muku ba, ko na dawo neman a zabe ni a karo na biyu, kar ku zabe ni.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: wutar lantarki yan Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
A yau Litinin ne tawagogin kasashen Sin da Amurka, suka sake tattaunawa a rana ta biyu, game da batutuwan tattalin arziki da cinikayya a birnin Madrid na kasar Sifaniya. A jiya Lahadi, sassan biyu sun gudanar da zaman farko ne a fadar Santa Cruz, inda ofishin ministan harkokin wajen kasar ta Sifaniya yake.
A cewar kakakin ma’aikatar cinikayyar kasar Sin, sassan biyu za su tattauna batutuwan da suka hada da matakin Amurka na kakaba jerin haraji daga bangare guda, da keta matakan kayyade fitar da hajoji, da batun dandalin TikTok. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp