Ya zargi gwamnatin da cewa ba ta dauki kwararan matakai na kawo babban gyara a fannin wutar lantarki ba, sannan ta gaza wajen nuna wani hobbasa game da lamarin ballantana har kuma ta dauki matakin gaggawa a cikin shekaru biyu da ta kwashe tana mulki.

“Mun wuce rabin lokacin wannan gwamnatin, kuma miliyoyin ‘yan Nijeriya na ci gaba da caji wayoyinsu a tashoshin caji na hannu, suna kashe dubban naira wajen sayen man fetur na janareta domin samun wutar lantarki.

“Ina hasken wutan lantarkin da aka yi wa ‘yan Nijeriya al’kawari? Me ya faru da alkawarinku? Kuma har yaushe ‘yan Nijeriya za su ci gaba da zama cikin duhu?”

Ya sake dawo wa da alkawarin Tinubu a lokacin yakin neman zabe, ya ce, “Mai Girma Shugaban Kasa, ka taba cewa, ‘Idan ban gyara wutar lantarki ba, ka da ku sake zabe na.’ Kuma ‘yan Nijeriya sun ji wannan. Za mu cika maka burinka a 2027.”

Bidiyon kamfen da Abdullahi yake yadawa a kafafen sadarwa na zamani, ya nuna inda Tinubu yake, “Zan bi duk wata hanyar na samur da cikakken wutar lantarki. Kuma ba za ku sake biyan kudin wutan lantarkin da ba ku shafa. Kyan alkawari cika. Idan ban cika alkawarin da na yi muku ba, ko na dawo neman a zabe ni a karo na biyu, kar ku zabe ni.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: wutar lantarki yan Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka: An gabatar da daftarin kudirin sake duba alaka da Afirka ta kudu

‘Yan majalisar dokokin Amurka sun gabatar da wani kudirin doka da ke ba da shawarar sake duba alakar Amurka da Afirka ta Kudu da kuma kakaba takunkumi a kan  wasu jami’ai da suka ki amincewa da manufofin Amurka na ketare.

Kwamitin harkokin wajen Amurka ya kada kuri’a don aikewa da daftarin kudiri a kan yin nazarin dangantakar Amurka da Afirka ta Kudu” zuwa ga babban zauren majalisar wakilai, inda za a kada kuri’a a kansa.

Wannan matakin na bukatar amincewa daga majalisun wakilai da na dattawa kafin ya zama doka, a cewar kamfanin dillancin labarai na Reuters.

‘Yar majalisar wakilai Ronny Jackson ce ta gabatar da kudirin dokar a watan Afrilun da ya gabata. Tana zargin Afirka ta Kudu da zagon kasa ga muradun Amurka ta hanyar kulla alaka ta kut da kut da Rasha da China, da kuma nuna adawa ga Isra’ila, gami  da kuma gurfanar da ita a gaban kotun kasa da kasa kan batun kisan gilla a a kan al’ummar Palasdinu.

Kudirin ya ba da shawarar yin cikakken nazari kan alakar kasashen biyu da kuma bayyana jami’an gwamnatin Afirka ta Kudu da shugabannin jam’iyyar ANC wadanda suka cancanci a kakaba musu takunkumi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4
  • Jihohin Da Ke Shirin Rage Kudin Wutar Lantarki Su Shirya Biyan Tallafi – Ministan Wuta
  • Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
  • Maraba Da Shekarar Hijirah Ta 1447: Manzon Allah (SAW) Zai Cika Shekara 1,500 Da Haihuwa A Shekarar (4)
  • Amurka: An gabatar da daftarin kudirin sake duba alaka da Afirka ta kudu
  • Tinubu ya fi mayar da hankali wajen gina Kudancin Nijeriya — Kwankwaso
  • Majalisar Dattawa Ta Amince Tinubu Ya Sake Ciyo Bashin Dala Biliyan 21 Daga Ƙetare
  • Tinubu ya sake miƙa buƙatar karɓo bashin Dala miliyan 347 daga ƙetare
  • Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin