Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Furuci Da Halakar Sojan Guda Da Ya Jikkata A Zirin Gaza
Published: 27th, July 2025 GMT
Sojojin mamayar Isra’ila sun yi furuci da halakar daya daga cikin sojojinsu sakamakon raunukan da ya samu a Zirin Gaza
Majiyar sojojin mamayar Isra’ila ta tabbatar a ranar Asabar din da ta gabata cewa: Wani soja ya mutu sakamakon raunukan da ya samu kwanakin baya -bayan nan sakamakon tashin bam a kan hanyar wata motar soji a zirin Gaza.
Tun da farko, sojojin mamayar Isra’ila sun amince da mutuwar Sajan Reserve Vladimir Loza, mai shekaru 36, daga matsugunin Ashkelon.
Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da ‘yan gwagwarmayar Falastinawa ke ci gaba da kai hare-hare da kuma kwantan bauna kan sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila a fagage da dama a zirin Gaza, lamarin da ya janyo hasarar rayuka da na dukiyoyi ga ‘yan mamayar.
A ‘yan kwanakin da suka gabata, rundunar sojin Qassam bangaren sojin kungiyar Hamas ta bayyana a ta bakin kakakinta, Abu Obeida, cewa: Dabarunta a wannan mataki ita ce ta “kokarin halaka makiya, da gudanar da hare-hare masu inganci, da kuma neman kame sojoji a matsayin fursunonin yaki.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: mamayar Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Mutane 6 Ne Suka Yi Shahada Sanadiyyar Hare-haren Yan Ta’adda A Zahidan
Wasu yan bindiga wadanda ake dangantasu da kungiyar Jaishul-Zulum sun dauki alhakin kai hare-hare a cikin wata kotu a birnin Zahidan babban birnin lardin Sistab Baluchistan a yau Asabar.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa yan ta’addan sun shigo da motarsu har zuwa a wata kotu a garin da Zahidan, sannan suka sauka suna son shiga kotun amma jami’an tsaro a kotun suka hanasu shiga. Daga nan kawai suka fara jefa nakiya irin da yaki a kansu.
An yi ta musayar wuta tsakaninsu da jami’an tsaro zuwa wani lokacin suka sami nasarar halakasu. Amma kuma sun kai mutane 6 ga shahada uku daga cikinsu jami’an tsaron kotun da kuma wani yaru da kuma wata mata yar kabilar Baluch wacce har yanzun ba’a ganeta ba.
Kungiyar yan ta’adda ta jaishul Zulum wacce take da cibiya a cikin yankin Baluchistan na kasar Pakisatan dai ta sha daukan alhakin kai hare-hare a yankin Sistan Baluchistan na kasar Iran. Tare da kashe Jami’an tsaro da kuma fararen hula, da kuma kawo hargitsi tsakanin mabiya mazhabobin musulunci daban –daban da kuma kabilu.
Mutane da dama sun ji rauni bayan wadanda suka yi shahada. Sannan mafi yawa an yi masu magani a asbitoci kuma an sallamesu.