Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ce sake gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 dole ne, ya taimaka wajen haɗa kan ƙasa, kyautata mulki, da bunƙasa tattalin arziƙi.

Ya buƙaci a gudanar da wannan aiki cikin adalci, gaskiya da kuma bisa ra’ayoyin jama’a gaba ɗaya.

HOTUNA: Shugaban Gambiya ya kai wa iyalan Buhari ziyarar ta’aziyya a Daura Za a ɗauke wuta na tsawon kwanaki 25 a Legas — TCN

Gwamna Abba, ya bayyana haka ne ta bakin Shugaban Ma’aikatansa, Sulaiman Wali.

Ya bayyana hakan ne lokacin da yake gabatar da saƙon maraba da baƙi a wajen Taron Sauraron Ra’ayoyin Jama’a na Yankin Arewa maso Yamma kan sake gyaran kundin tsarin mulki, da aka gudanar a Kano ranar Asabar.

Yayin da yake maraba da kwamitin Majalisar Dattawa da sauran baƙi, gwamnan, ya ce wannan taro muhimmin mataki ne ga ci gaban dimokuraɗiyyar Najeriya.

“Yana da muhimmanci na tarbe ku zuwa Jihar Kano, mambobin kwamitin Majalisar Dattawa kan sake gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya, domin wannan muhimmin aiki na ƙasa.

“Haka kuma muna maraba da ‘yan ƙasa da sauran masu ruwa da tsaki da suka halarta domin tattauna makomar ƙasarmu.

“Muna alfahari da cewa Kano, jiha mai yawan jama’a da tarihin siyasa, ce ke karɓar wannan gagarumin taro,” in ji shi.

Gwamnan, ya ce wannan taro na zuwa a lokacin da ya dace, kuma zai bai wa ‘yan Najeriya damar bayar da gudunmawa wajen tsara dokokin da za su tafiyar da ƙasar.

“Wannan taro yana nuna yadda muke jajircewa wajen ƙarfafa gwamnati mai nagarta da kuma gina ƙasa mai adalci da ƙwarewar shugabanci,” a cewarsa.

Ya bayyana kundin tsarin mulki a matsayin ginshiƙi da tushen kowace gwamnati.

“Kundin tsarin mulki shi ne zuciyar tsarin mulkin kowace ƙasa. Shi ne jagoran adalci da ginshiƙi a wajen jama’a.

“Shi ke ƙayyade dangantaka tsakanin gwamnati da jama’a. Saboda haka, dole a gudanar da sake gyaranss cikin gaskiya da adalci,” in ji shi.

Gwamna Abba, ya kuma ne dole a tabbatar da cewa wannan sabon tsarin zai amfani kowa da kowa; daga Arewa zuwa Kudu, maza da mata, matasa da tsofaffi.

“Wannan sabon tsarin ya zama wanda zai haɗa ƙasa, ya kyautata shugabanci, ya kuma bunƙasa tattalin arziƙi. Duk wani gyara da za a yi ya zama wanda zai dace da burin jama’a da halin da ake ciki yanzu,” in ji shi.

Ya ambaci wani lauya a Amurka mai suna Cameron Smith, wanda ya jaddada muhimmancin gaskiya da riƙon amana a cikin gwamnati.

“Dole ne mu kafa ƙa’idojin da za su bai wa kowa dama, rage rikice-rikice, da kuma samar da tsarin tarayya na gaskiya da adalci,” a cewarsa.

Ya kuma yaba da jagorancin Majalisar Tarayya da kwamitin sake gyaran kundin tsarin mulki saboda fara wannan muhimmin aiki, kuma ya bukaci a gudanar da shi cikin gaskiya da adalci.

“Ina roƙon kwamitin da ya tabbatar da cewa aikin yana tafiya cikin gaskiya tare da nufin karfafa zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban ƙasa,” in ji shi.

Ya kuma shawarci kwamitin da ya kasance bisa doron gaskiya da kishin ƙasa.

“Wannan lokaci ne na haɗin kai, ba na raba kawuna ba. Lokaci ne na kafa ginshiƙai domin gina Najeriya da kowa zai amfana da ita, ba tare da la’akari da addini, ƙabila ko asali ba.

“Dole mu yi abin da zai haɗa kan al’umma, ya kawo adalci, da kuma bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa,” in ji shi.

Yayin da yake bayani kan rawar da Kano ke takawa a tsarin, gwamnan ya ce sun yi taruka da dama da al’umma, kuma za su miƙa cikakken rahoto nan ba da jimawa ba.

“Matsayin da Kano ke kai a wannan aiki ya samu ne daga haɗin gwiwa da jama’a, kuma muna shirin miƙa rahoton da ke ɗauke da ra’ayoyin al’ummar Jihar Kano,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gwamna Abba gyara Kundin tsarin mulki Kwamiti Majalisar Dattawa Ra ayin jama a taro sake gyaran kundin tsarin mulki

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano

Hukumar Kula da Inshorar Lafiya ta Kasa (NHIA) a ranar Laraba ta kaddamar da shirin bayar da kulawar lafiyar gaggawa kyauta ga yara a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH), Kano.

Shirin, a cewar Darakta a hukumar, Dr. Salahudeen Sikiru, wani bangare ne na fadada shirin lafiyar iyaye da NHIA ke aiwatarwa zuwa ga yara masu rauni da masu bukata ta musamman.

Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo Ana zargin mace da kashe ’yar uwarta a kan N800 din barkono

Ya ce an fara shirin fiye da shekara ɗaya da ta gabata da nufin rage mace-macen jarirai ’yan kasa da shekaru biyar.

“Mun fara wannan shiri fiye da shekara guda da ta gabata da nufin rage mace-macen jarirai. Yanzu mun zo nan don fara na ɓangaren jarirai. Mu za mu biya kudin kulawar gaggawar yaran sannan mu tabbatar an kula da su har su samu ingantacciyar lafiya,” in ji Dr. Sikiru.

Ya kuma ce a karkashin shirin, yara da ke fama da matsalolin gaggawa kamar rashin numfashi, amosanin jini, cutar shawara da yaran da aka haifa bakwaini da ma cututtukan da ke buƙatar tiyata za su samu kulawa kyauta.

Ya ce asibitoci za su fara ba da kulawa da zarar an kawo yara, sannan su tura adadin kuɗin kula da yaran a kowanne mako ga NHIA don a biya su.

Daraktan ya kara da cewa duk yaran da ya sami kulawar gaggawar kuma, za a saka shi cikin shirin inshorar lafiya na NHIS, inda hukumar za ta ci gaba da biyan kudin inshorar don tabbatar da samun kulawar lafiya mai inganci.

“Kafin yaro ya ci gajiyar shirin, dole ne a tantance shi a a tabbatar yana da rauni da kuma ba zai iya biyan kuɗin asibiti ba. Haka nan dole ne yaro ya mallaki Lambar Shaida ta Kasa (NIN) don tabbatar da gaskiya da shigar da su cikin tsarin,” in ji shi.

Dr. Sikiru ya kuma ce, “Shiri ne kula da marasa lafiya cikin gaggawan. Da zarar sun zo, za a duba su. Asibitin sai ya turo mana jimillar adadin kudin, mu kuma mu biya.”

Ya ce wannan shiri wani bangare ne na kudurin gwamnatin tarayya na rage mace-macen jarirai da tabbatar da cewa babu yaron da ya rasa kulawar asibiti saboda rashin kudi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Sabon Tsarin Kula Da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu Da Kananan Yara
  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • Za A Kada Kuri’ar Raba Gardama Akan Sabon Tsarin Mulki A Kasar Guinea
  • Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya
  • Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu Kano
  • Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Mayar Wa Atiku Martani Kan Cewar ‘Yan Nijeriya Na Fama Da Yunwa
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja