Dole gyaran kundin tsarin mulki ya haɗa kan ƙasa da shugabanci na gari — Abba
Published: 26th, July 2025 GMT
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ce sake gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999 dole ne, ya taimaka wajen haɗa kan ƙasa, kyautata mulki, da bunƙasa tattalin arziƙi.
Ya buƙaci a gudanar da wannan aiki cikin adalci, gaskiya da kuma bisa ra’ayoyin jama’a gaba ɗaya.
HOTUNA: Shugaban Gambiya ya kai wa iyalan Buhari ziyarar ta’aziyya a Daura Za a ɗauke wuta na tsawon kwanaki 25 a Legas — TCNGwamna Abba, ya bayyana haka ne ta bakin Shugaban Ma’aikatansa, Sulaiman Wali.
Ya bayyana hakan ne lokacin da yake gabatar da saƙon maraba da baƙi a wajen Taron Sauraron Ra’ayoyin Jama’a na Yankin Arewa maso Yamma kan sake gyaran kundin tsarin mulki, da aka gudanar a Kano ranar Asabar.
Yayin da yake maraba da kwamitin Majalisar Dattawa da sauran baƙi, gwamnan, ya ce wannan taro muhimmin mataki ne ga ci gaban dimokuraɗiyyar Najeriya.
“Yana da muhimmanci na tarbe ku zuwa Jihar Kano, mambobin kwamitin Majalisar Dattawa kan sake gyaran kundin tsarin mulkin Najeriya, domin wannan muhimmin aiki na ƙasa.
“Haka kuma muna maraba da ‘yan ƙasa da sauran masu ruwa da tsaki da suka halarta domin tattauna makomar ƙasarmu.
“Muna alfahari da cewa Kano, jiha mai yawan jama’a da tarihin siyasa, ce ke karɓar wannan gagarumin taro,” in ji shi.
Gwamnan, ya ce wannan taro na zuwa a lokacin da ya dace, kuma zai bai wa ‘yan Najeriya damar bayar da gudunmawa wajen tsara dokokin da za su tafiyar da ƙasar.
“Wannan taro yana nuna yadda muke jajircewa wajen ƙarfafa gwamnati mai nagarta da kuma gina ƙasa mai adalci da ƙwarewar shugabanci,” a cewarsa.
Ya bayyana kundin tsarin mulki a matsayin ginshiƙi da tushen kowace gwamnati.
“Kundin tsarin mulki shi ne zuciyar tsarin mulkin kowace ƙasa. Shi ne jagoran adalci da ginshiƙi a wajen jama’a.
“Shi ke ƙayyade dangantaka tsakanin gwamnati da jama’a. Saboda haka, dole a gudanar da sake gyaranss cikin gaskiya da adalci,” in ji shi.
Gwamna Abba, ya kuma ne dole a tabbatar da cewa wannan sabon tsarin zai amfani kowa da kowa; daga Arewa zuwa Kudu, maza da mata, matasa da tsofaffi.
“Wannan sabon tsarin ya zama wanda zai haɗa ƙasa, ya kyautata shugabanci, ya kuma bunƙasa tattalin arziƙi. Duk wani gyara da za a yi ya zama wanda zai dace da burin jama’a da halin da ake ciki yanzu,” in ji shi.
Ya ambaci wani lauya a Amurka mai suna Cameron Smith, wanda ya jaddada muhimmancin gaskiya da riƙon amana a cikin gwamnati.
“Dole ne mu kafa ƙa’idojin da za su bai wa kowa dama, rage rikice-rikice, da kuma samar da tsarin tarayya na gaskiya da adalci,” a cewarsa.
Ya kuma yaba da jagorancin Majalisar Tarayya da kwamitin sake gyaran kundin tsarin mulki saboda fara wannan muhimmin aiki, kuma ya bukaci a gudanar da shi cikin gaskiya da adalci.
“Ina roƙon kwamitin da ya tabbatar da cewa aikin yana tafiya cikin gaskiya tare da nufin karfafa zaman lafiya, haɗin kai da ci gaban ƙasa,” in ji shi.
Ya kuma shawarci kwamitin da ya kasance bisa doron gaskiya da kishin ƙasa.
“Wannan lokaci ne na haɗin kai, ba na raba kawuna ba. Lokaci ne na kafa ginshiƙai domin gina Najeriya da kowa zai amfana da ita, ba tare da la’akari da addini, ƙabila ko asali ba.
“Dole mu yi abin da zai haɗa kan al’umma, ya kawo adalci, da kuma bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa,” in ji shi.
Yayin da yake bayani kan rawar da Kano ke takawa a tsarin, gwamnan ya ce sun yi taruka da dama da al’umma, kuma za su miƙa cikakken rahoto nan ba da jimawa ba.
“Matsayin da Kano ke kai a wannan aiki ya samu ne daga haɗin gwiwa da jama’a, kuma muna shirin miƙa rahoton da ke ɗauke da ra’ayoyin al’ummar Jihar Kano,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamna Abba gyara Kundin tsarin mulki Kwamiti Majalisar Dattawa Ra ayin jama a taro sake gyaran kundin tsarin mulki
এছাড়াও পড়ুন:
Ina Karanta Rantsuwar Da Na Yi A Kullum Don Tuna Nauyin Da Ke Kaina-Gwamna Namadi
Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya bayyana cewa yana yawan karanta rantsuwar kama aiki da ya yi domin tunatar da kansa nauyin da ya dauka na yi wa al’umma hidima bisa gaskiya da amana.
Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamna, Hamisu Mohammed Gumel, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba bayan nadin sabon shugaban karamar hukumar Gumel.
A wajen bikin da aka gudanar a zauren majalisar gwamnatin jihar da ke Dutse, Gwamna Namadi ya yi nuni da cewa rayuwa na da kurarran lokaci, don haka ya kamata shugabanni su kasance masu tsoron Allah da kuma sanin nauyin da ke kansu.
“Rayuwa ba ta da tabbas, hakazalika shugabanci ba wasa ba ne”. In ji shi.
Ya bukaci masu rike da madafun iko da su kasance masu kula da al’amuransu cikin tsoron Allah da sanin cewa akwai ranar hisabi da mutuwa.
Da yake jawabi ga sabon shugaban karamar hukumar, Gwamnan ya ce: “Rantsuwar da ka dauka ita ce mu ma muka dauka. Na ajiye tamu a kan teburi a ofishina, kuma kullum ina karanta ta. Ina ba ka shawarar kai ma ka rika karanta taka kafin ka fara aiki a kullum.”
Ya ja hankalin sabon shugaban da kada ya bari son zuciya ya shige masa gaba wajen gudanar da ayyukansa, yana mai cewa son kai na daga cikin manyan matsalolin da ke gurgunta mulki mai nagarta.
Ya bukaci sabon shugaban da ya yi aiki da kowa, ya rika tuntubar masu ruwa da tsaki, tare da sanya mutanen da ya ke wakilta gaba a kowanne lokaci.
Gwamnan ya kammala da cewa shugabanci yana bukatar hakuri, kwarewa, da tsoron Allah, yana mai cewa“babu wanda aka haifa da basirar shugabanci, amma da kaskantar da kai da tsoron Allah, za ka yi nasara”
Usman Muhammad Zaria