Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana
Published: 27th, July 2025 GMT
Ma’aikatar kula da sashen ayyukan jigilar kayayyaki ta kasar Sin ta ba da rahoton cewa, a cikin rabin farkon bana, an samu ci gaba mai yawa a bangaren, kamar yadda alkaluman hukuma suka nuna a jiya Lahadi.
Hukumar raya ci gaban kasa da gudanar da gyare-gyare, wacce take da alhakin tsara tsare-tsaren tattalin arzikin kasa ta yi bayanin cewa, kudin da ake kashewa a ayyukan jigilar kaya ya kai kaso 14 cikin dari na GDPn kasar a watanni shida na farkon shekarar, inda ya ragu da kaso 0.
A cewar hukumar, wannan na nuni ne da sakamakon farko da aka samu wajen rage tsadar ayyukan a cikin al’umma. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Manyan Nasarorin Da Dakta Dantsoho Ya Samar Tun Darewarsa Shugabancin NPA
Wani abin karin farin ciki shi ne, yadda masu rauwa da tsaki a fannin, suka jinjinawa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, kan yadda ya zabo ya kuma nada Dantsoho, a matsayin shugaban NPA, inda akasarin su, suka yi ittifakin cewa, zabo, bai zama zabar Tumun dare ba, musamman duba da irin dimbin ci gaban da yake ci gaba da samar wa a fannin, a cikin shekara daya kacal.
Gyaran Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar:
Tun bayan da ya dare karagar shugabancin NPA Dantsho ya lashi Takon, inganta ayyukan Tashoshin, inda ka fara da tattara bayanan ayyukan da ya kamata ayi da kuma fara yin aikin gadan-gadan, inda aka ware dala bilyan daya, domin fara gyran Tashar Tincan Island, ta Apapa, ta Onne da ke jihar Ribas, ta Warri da kuma ta Kalaba.
Aikin Fadada Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar:
A karkashin shugabancin na Dantsoho na NPA, ya dauki sabbin kwararan matakai domin fadada ayyukan na NPA, inda a watan da ya gabata, Dantsoho, ya jagoranci tawagar sauran mahukuntan NPA, kan rattaba hannun yarjejeniyar, dala biliyan daya don bunkasa aikin Tashar Snake Island, don a samar da hekta guda 85, don gudanar da hada-hadar shiyya ta shige da ficen Jiragen Ruwa.
Kazalika, akwai kuma aikin Tashoshin Badagry na Ondo da kuma na Burutu, wadanda a yanzu, suka kai matakin kammala wa.
Samar Da Kyakyawan Tsarin Ajiye Kwantaina A Tashshin Jiragen Ruwa:
A karkashin shugabancin sa, NPA ta zama mamba a kungiyar IPCSA, wanda hakan, ya bai wa kasar damar wanzar da aikin NSW.
Dantsoho, ya tabatar da an samar da tsarin gudanar da ayyuka na bai daya, wato NSW wanda shi ne, ake gudanarwa, a daukacin fadin duniya, musamman wajen samun musayara bayanai, na zirga-zirgar kayan da Jirage suka yo dakon su, ko dai ta ruwa, ko ta sama ko kan tudu.
Yin Amfani Da Na’urori Don Magance Cunkoson Motoci A Tashoshin Jiragen Ruwa:
Kirkiro da yain amfani da na’urorin rage cunkoson motocin da ke shiga cikin Tashoshin Jiragen Ruwan kasa, da a karkashin shugabancin Dantsoho, hakan ya taimaka matuka wajen rage cunkoso a daukacin Tashoshin kasar, musamman duba da yadda, aka samar da guraren da za a rinka ajiye motocin.
Kazalika, an yi hakan ne, domin a samar saukin gudanar da hada-hadar kasuwanci ta yau da kullum a Tashoshin.
Kara Bunkasar Fitar Da Kaya Ketare Da Habakar Kasuwanci:
Sakamakon kara inganta Tashoshin Jiragen Ruwan kasar a karkashin shugabancin Dantosho, hakan ya sanya hada-hadar kasuwancin kasar, a zango na uku na 2024, Nijeriya ta samu Naira tiriliyan 5.81 wadanda suka yi, daidai da dala bilyan 3.7.
Bugu da kari, bisa nasarar da aka samu ta wanzar da tsarin sayar da Danyen Mai da sauran Dangogin Mai kan farashin Naira, da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya bayar da umarnin a yi, hakan ya sanya, Nijeriya ta samu damar adana biliyoyin kudaden musaya na kasar waje.
Kazalika, hakan ya sanya, an rage dogaro da shigo Man daga waje, wanda kuma hakan ya kara yawan albarkatun makamashi na kasar, tare da samar da ayyukan yi, na kai tsaye, da wadanda ba na kai tsaye ba.
Hakazalika, a Hukumar NPA a karashin shugabancin Dantsoho, ta sanya batun hadaka da kamfanoni masu zaman kansu wato kan tsarin PPP, wanda hakan ya kara yawan kudaden shigar da take Tarawa.
Shigar Nijeriya Cikin Kungiyar Kula Da Tashoshin Jiragen Ruwa Ta PMAWCA
A lokacin shugabancin sa ne, Nijeriya ta shiga cikin sahun sauran kasashen da ke Afirka ta Yamma na sufurin Jiragen Ruwa, inda aka zabi Dantsoho a matsayin Shugaban kungiyar kula da Tashoshin Jiragen Ruwa na Afirka Yamma wato PMAWCA.
Kazalika, ta hanyar zabar sa ne, ya sanya tun bayan kafa kungiyar a 1972 aka samu dan Nijeriya na farko, da zama Shugaban kungiyar.
NPA ta taimaka matuka, wajen samar da shawarari kan kara yawan sufurin Jiragen Ruwa daga Tashar Lekki, zuwa sauran kasashen, da ke makwabtaka, da Nijeriya.
Kara Samar Da Masu Zuba Hannun Jari:
Duba da irin kwarewar da ya samu, musamman a lokacin da ya rike mukamin Manaja na Tashar Onne, wanda a lokacin ya samar da huddar abotakar kasuwanci a Tashar ta Onne, a kwanna baya Dantsoho ya kai ziyarar aiki, a Tashoshin NPA da ke a Gabashin kasar, musamman idan ya nuna bukatar samar da masu son zuba hannun jari, a Tashohin Ribas, Kalaba da ta Burutu.
Hakan ya sanya, kamfanonin da ke yin dakon Kwantainoni, musamman na yankin Yammacin Afirka wato WACT-APM, suka kadammar da ayyukansu.
Kazalika, an gudanar da aikin ne, bisa hadaka da kamfanin Hapag-Lloyd.
Hakan ya kuma kara bunkasa hada-ahadar kasuwanci a kan lokaci, musamman ga Jiragen da ke sauka a gabashin kasar.
Rahoton Kididdigar Ayyuaka A NPA:
Bisa rahoton kididdiga na mahkuntan NPA a 2024, ya nuna cewa, an samu gagarumar ci gaba a bangarori da ban da ban a NPA, wadanda suka hada da; gudanar da ayyuakn zirga-zirgar kananan Jiragen Ruwa da sauransu.
A 2024, NPA ta kara samun yawan Jiragen dakon kaya da ke zuwa Tashoshin Jiragen ruwan kasar, inda suka karu daga kaso kaso 45.1 zuwa kaso 71,213,197, wanda kuma hakan ya nuna cewa, yawan hada-hadar kasuwancin da aka gudanar, sun kara ayyukan na NPA.
Jiragen da ke tsaya wa a Tashar Lekki, sun karu zuwa kaso 2,160.8, inda kuma wadanda ke tsayaw a Tashar Onne, suka karu zuwa kaso 9.4%, sai kuma na Tashar Tin Can Island, da suka karu zuwa kaso 7.3.
Samun Karin Jiragen Ruwa Da Ke Zuwa Tashoshin Jiragen Ruwan Kasar:
Yawan Jiragen Ruwa da ke zuwa Tashoshin sun karu daga kaso 5.6 zuwa kaso 3,791 a 2023, inda kuma a 2024, suka karu zuwa kaso 4,005.
Hakan ya nuna yadda aka samu karin yawan masu yin rijista da suka kai, karin kaso 15.4, wanda hakn yah aura, daga tan na kaya 123,660,278 zuwa tan to142,660,418.
Tashar Lekki ta kasance kan gaba, inda aka yi rijistar Jiragen da ke zuwa Tashar suka karu zuwa kaso 477.6, sai ta Onne, ta samu karin kaso 5.8.
Jimlar Kwantainoni da ake sauke wa a Tashar sun karu zuwa kaso 9.7 a 2024, idan aka kwatatan da na 2023.
Kazalika, karin Kwantaononin da ke fitar da su, sun karu zuwa 53.7 daga kaso 12.2.
Bugu da kari, yawan sauran Kwantainonin da ke fitar da su, sun karu zuwa kaso 136.5.
Zirga-Zirgar Kananan Jiragen Ruwa Ta Karu:
Ayyukan zirga-zirgar kanannan Jiragen Ruwa a Tashoshin Jiragenn Ruwan kasar, ya karu zuwa kaso 49.6, inda kuma yawan Jiragen daga 8,956 da ake yin amfani da su a 2023, suka karu zuwa 13,396 a 2024.
Hakazalika, karin wadanda suka yi rijista na GRT, sun karu daga kaso 129.3 zuwa kaso 1,997,163 sai kuma wani karin kaso 4,579,742.
Dantsho ya tabatar da ya daidaita iya lokacin zuwan Jiragen Ruwa ga Tashoshin da kuma lokacin da ya kamata su juya, musamman domin a rage cunkoson Jiragen Ruwa a Tashohin wanda wanda hakan ya sanya aka samu gudanar da ayyuka a Tashoshin da suka kai kaso 1.0.
Musamman a Tashar Lekki wadda ta kasance a cikin kwanuka 2.5 kacal, ake samun Jiragen da ke zuwa suna kuma juyawa, bayan sun sauke kayan da suka yi dako.
Yawan lokutan zuwa da juyawar Jiragen a 2023, ya kai kaso 30.1, wanda a 2024, ya karu zuwa kaso 33.
Tabbara Da Walwala Da Jin Dadin Ma’aikata:
Dantsoho ya mayar da hankali wajen inganta jin dadi da walwalar ma’aikan NPA a matsayin daya daga cikin muradun shugabancinsa, musamman ta hanyar yin hadaka da kunyoyin ma’aikatan irinsu, MWUN da kuma SSASGOC.
Hakan ya sanya, kungiyoyin suka kuma yabawa Ministan Bunkasa Tattalin Arziki na Ruwa Adegboyega Oyetola da kuma Dantsoho saboda kawo karshen matsalolin da suka dakele su, na samun ci gaban da ya kamata su samu da sauransu, musamman samun jarrabawar karin girma, a NPA.
Samun Jinjina Da Yabo:
Hatta daga gun Dangote da sauran masu ruwa da tsaki da kuma sauran kamfanoni, Dantsoho ya samu yabon su da kuma jinjinar su saboda irin irin kokrin da yake yi na ciyar da NPA gaba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp