Shugaban Kasar Amurka Ya Shiga Cikin Sahun Masu Mafarkin Rusa Kungiyar Hamas
Published: 27th, July 2025 GMT
Shugaban kasar Amurka ya shiga sahun masu mafarkin zasu rusa kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas da ke Falasdinu
Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi barazanar kawar da kungiyar Hamas idan har ba a cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta ba, yana mai zargin kungiyar da rashin son cimma matsaya.
Da alama mai shiga tsakani na Amurka ya yanke shawarar jagorantar kai farmakin da gwamnatin mamayar Isra’ila ke kaiwa Gaza, inda shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana aniyarsa ta kawar da kungiyar Hamas. Ya yi ikirarin cewa: Kungiyar Hamas ba ta son cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta a Gaza, yana mai imanin cewa; Hamas ba ta son kawo karshen yakin saboda ta san abin da zai faru bayan ta saki fursunonin da suke hannunta. Wannan bayani ya bayyana aniyar ci gaba da yakin, ko da kuwa da yarjejeniyar tsagaita wuta. Duk da amincewar da Trump ya yi na wahala wajen kwato sauran fursunonin, ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta jaddada cewa; Trump da sakataren harkokin wajen Amurka, Marco Rubio, sun dukufa wajen ganin an sako fursunonin.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kungiyar Hamas
এছাড়াও পড়ুন:
Ruwa da iska sun kashe mutum 5, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
Ruwan sama kamar da bakin kwarya hade da iska sun yi ajalin mutum biyar sannan wasu 92 suka samu munanan raunuka a kananan hukumomi bakwai na jihar Yobe.
Shugaban Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (SEMA) Dr Goje ne ya tabbatar da hakan a ranar Laraba a Damaturu.
Ya ce iftila’in ya shafi al’ummomi 48 ne a fadin kananan hukumomin da lamarin ya faru.
Matar aure ta kashe mijinta a kan abinci a Yobe Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka saceDr Goje yan kuma ce bala’in ya shafi gidaje 1,264, tare da raba mutum 5,022 da muhallansu.
Shugaban ya kuma ce hukumarsa tare da hadin gwiwar kungiyar bayar da tallafi ta kasa da kasa ACF tare da tallafi daga ofishin kula da harkokin wajen Jamus (GFFO), sun raba kayan agajin ceton rai ga magidanta 566 a kananan hukumomin Fika da Potiskum da lamarin ya shafa.
Kazalika, kididdigar haɗin gwiwa ta hukumar ta SEMA da ACF suka fitar ta ba da fifiko ga iyalan da wadanda wannan iftila’i ya fi shafa kai tsaye musamman waɗanda suka rasa gidajensu, da kayan masarufi, ko damar samun wani taimakon na tsafta.
Mohammed Liman Kingimi, na kungiyar ACF, ya tabbatar da kudurin kungiyar na kara ba da taimako bisa ga yadda bukatun hakan suka taso.
Ya ce kungiyar na kuma shirye-shiryen kaddamar da tallafin abinci ga magidanta 566 don rage musu radadi.
Dokta Goje ya buqaci wadanda suka ci gajiyar tallafin da su yi amfani da shi yadda ya kamata sannan ya jaddada kudirin gwamnatin jihar na kare al’umma masu rauni ta hanyar xaukar matakan gaggawa.
Ya kuma jaddada qudirin hukumar cewa kullum a shirye take wajen gudanar da ayyukanta kamar yadda ya dace.