Aminiya:
2025-07-27@04:38:23 GMT

ADC ce kaɗai za ta iya magance matsalolin Arewa — David Mark

Published: 27th, July 2025 GMT

Shugaban riƙon ƙwarya na jam’iyyar ADC, David Mark, ya ce Arewacin Najeriya na cikin mawuyacin hali, kuma jam’iyyarsu ce kaɗai za ta iya warware waɗannan matsaloli idan aka zaɓe ta.

Ya bayyana hakan ne a taron jam’iyyar ADC da aka yi a Abuja Continental Hotel, inda mambobi da magoya bayan jam’iyyar daga sassa daban-daban suka halarta.

Dole gyaran kundin tsarin mulki ya haɗa kan ƙasa da shugabanci na gari — Abba Za a ɗauke wuta na tsawon kwanaki 25 a Legas — TCN

David Mark, wanda tsohon Shugaban Majalisar Dattawa ne, ya gabatar da jawabi mai taken: “Haɗin kai da zaman lafiya su ne mafita ga matsalolin Arewa”.

Ya ce Arewa na fuskantar matsaloli masu tsanani kamar su rashin tsaro, talauci, rikicin ƙabilanci da addini, rikicin siyasa da kuma durƙushewar tattalin arziƙi da zamantakewa.

Ya ce, “Waɗannan matsaloli ba yau aka fara su ba, kuma ba za su gushe ba sai mun tashi tsaye tare da ɗaukar matakai na gaskiya da haɗin kai.

“Dole ne mu karɓi gaskiya cewa mu ne muke da hannu a cikin matsalolinmu. Ka da mu ci gaba da ɗora laifi kan wasu idan muna so mu samu mafita ta gaskiya.”

Ya ƙara da cewa yin shiru kan matsalolin na ƙara dagula lamarin.

Ya buƙaci al’ummar Arewa su koma kan ɗabi’unsu na adalci, daidaito, mutunta juna da yin aiki tare, waɗanda suka sa Arewa ta zama abar koyi wajen zaman lafiya da ci gaba.

“Lokacin koke-koke ya wuce,” in ji shi.

“Arewa na zubar da jini, kuma mu kaɗai ne za mu iya warkar da ita. Mu guji kalaman ƙiyayya da siyasar raba kawuna. Mu mayar da hankali kan abubuwan da za su haɗa mu waje ɗaya; ilimi da lafiya.

“Mu kuma riƙa ɗaukar alhakin abubuwan da muka yi ko muka kasa yi, sannan mu haɗa hannu domin dawo da zumunci da haɗin kanmu.”

Ya ce idan aka yi haka, za a iya sake gina Arewa ta zama cibiyar zaman lafiya, fahimta da ci gaban tattalin arziƙi da fasaha.

David Mark, ya nuna damuwa kan yadda ’yan bindiga, ’yan ta’adda da rikicin ƙabilanci suka mayar da wasu ƙauyuka a Arewa tamkar wuraren yaƙi.

A cewarsa miliyoyin mutane sun rasa matsuguni, kuma tattalin arziƙin yankin ya durƙushe.

Ya ƙara da cewa duk da albarkatu masu tarin yawa da Arewa ke da su, ita ce mafi talauci a Najeriya, inda jahilci, rashin aikin yi da rashin ababen more rayuwa suka yi yawa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa David Marl Zaɓe

এছাড়াও পড়ুন:

Faransa Zata Bayyana Amincewa Da Samuwar kasar falasdinu

Shugaban kasar faransa Emanuel macron ya bayyana a jiya Alhamis kan cewa zai shelanta amincewar gwamnatin kasar Faransa da samuwar kasar falasdinu mai cikekken iko a taron babban zauren MDD a cikin watan satumba mai zuwa.

Jaridar ‘Arabnews’ ta kasar saudiya ta nakalto macron yana fadar haka a shafinsa na X ‘ ya kuma kara da cewa, da farko yana son ganin yaki a gaza ya zo karshe, sannan fararen hula da suke gaza su tsira daga kisa da kuma yunwan da aka dora masu.

Kasar faransa dai ita ce babbar kasa a cikin kasashen turai da suka fara amincewa da kasar Falasdinu mai zaman kanta. Kafin haka dai kasashen 140 a duniya sun amince da samuwar kasar falasdinu mai zaman kanta.

A jiya Alhamis gwamnatin kasar faransa a hukumance ta mikawa mataimakin shugaban PLO a birnin Qudus Hussain Al-sheikh. Shugaba Mahmood Abbas yay aba da matsayin da shugaban kasar faransa ya dauka ya kuma gode masa da wannan kokarin.

Kamar yadda aka saba, HKI ta yi allawadai da matsayin na shugaba macron. Haka ma Marco Rubio

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsofaffin Gwamnoni Sun Ziyarci Tinubu Tare Da Bashi Shawarwari Kan Matsalolin Tsaro
  • Mutanen A Netherlands Suna Zaman Dirshen Saboda Gaza
  • Faransa Zata Bayyana Amincewa Da Samuwar kasar falasdinu
  • HOTUNA: Yadda Kwankwaso ya karɓi ’yan APC zuwa NNPP a Kano
  • Kwankwaso Ya Soki Gwamnatin Tinubu Kan Ware Arewacin Nijeriya A Rabon Arzikin Ƙasa
  • Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja
  • Ɓullar Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja
  • Ministan Lafiya Na Kamaru: Hadin-Gwiwa Ta Fuskar Kiwon Lafiya Ta Shaida Zumunci Mai Karfi Tsakanin Kamaru Da Sin
  • NAJERIYA A YAU: Cututtukan da rumar daki ke haifarwa ga jikin mutum