ADC ce kaɗai za ta iya magance matsalolin Arewa — David Mark
Published: 27th, July 2025 GMT
Shugaban riƙon ƙwarya na jam’iyyar ADC, David Mark, ya ce Arewacin Najeriya na cikin mawuyacin hali, kuma jam’iyyarsu ce kaɗai za ta iya warware waɗannan matsaloli idan aka zaɓe ta.
Ya bayyana hakan ne a taron jam’iyyar ADC da aka yi a Abuja Continental Hotel, inda mambobi da magoya bayan jam’iyyar daga sassa daban-daban suka halarta.
David Mark, wanda tsohon Shugaban Majalisar Dattawa ne, ya gabatar da jawabi mai taken: “Haɗin kai da zaman lafiya su ne mafita ga matsalolin Arewa”.
Ya ce Arewa na fuskantar matsaloli masu tsanani kamar su rashin tsaro, talauci, rikicin ƙabilanci da addini, rikicin siyasa da kuma durƙushewar tattalin arziƙi da zamantakewa.
Ya ce, “Waɗannan matsaloli ba yau aka fara su ba, kuma ba za su gushe ba sai mun tashi tsaye tare da ɗaukar matakai na gaskiya da haɗin kai.
“Dole ne mu karɓi gaskiya cewa mu ne muke da hannu a cikin matsalolinmu. Ka da mu ci gaba da ɗora laifi kan wasu idan muna so mu samu mafita ta gaskiya.”
Ya ƙara da cewa yin shiru kan matsalolin na ƙara dagula lamarin.
Ya buƙaci al’ummar Arewa su koma kan ɗabi’unsu na adalci, daidaito, mutunta juna da yin aiki tare, waɗanda suka sa Arewa ta zama abar koyi wajen zaman lafiya da ci gaba.
“Lokacin koke-koke ya wuce,” in ji shi.
“Arewa na zubar da jini, kuma mu kaɗai ne za mu iya warkar da ita. Mu guji kalaman ƙiyayya da siyasar raba kawuna. Mu mayar da hankali kan abubuwan da za su haɗa mu waje ɗaya; ilimi da lafiya.
“Mu kuma riƙa ɗaukar alhakin abubuwan da muka yi ko muka kasa yi, sannan mu haɗa hannu domin dawo da zumunci da haɗin kanmu.”
Ya ce idan aka yi haka, za a iya sake gina Arewa ta zama cibiyar zaman lafiya, fahimta da ci gaban tattalin arziƙi da fasaha.
David Mark, ya nuna damuwa kan yadda ’yan bindiga, ’yan ta’adda da rikicin ƙabilanci suka mayar da wasu ƙauyuka a Arewa tamkar wuraren yaƙi.
A cewarsa miliyoyin mutane sun rasa matsuguni, kuma tattalin arziƙin yankin ya durƙushe.
Ya ƙara da cewa duk da albarkatu masu tarin yawa da Arewa ke da su, ita ce mafi talauci a Najeriya, inda jahilci, rashin aikin yi da rashin ababen more rayuwa suka yi yawa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa David Marl Zaɓe
এছাড়াও পড়ুন:
NECO ta saki sakamakon jarabawar 2025
Hukumar Shirya Jarabawa ta Ƙasa (NECO), ta fitar da sakamakon jarabawar kammala sakandare (SSCE) na shekarar 2025.
Daga cikin ɗaliban da suka zana jarabawar guda 818,492, kashi 60.26 sun ci aƙalla darusa biyar da suka haɗa da Lissafi da Turanci.
Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi Gwamnati ta fara duba yara marasa galihu kyauta a asibitin Aminu KanoShugaban NECO, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi, ya ce ɗalibai 1,367,210 suka yi rajistar jarabawar; maza 685,514 da kuma mata 681,696.
Amma daga cikinsu, ɗalibai 1,358,339 ne suka zana jarabawar.
Ya ce ɗalibai 1,144,496, wanda ya kai adadin kashi 84.26, sun samu darusa biyar ba tare da cin Lissafi da Turanci ba.
Sai dai an dakatar da sakin sakamakon makarantu takwas a Ƙaramar Hukumar Lamorde ta Jihar Adamawa saboda rikicin ƙabilanci da ya auku tsakanin 7 zuwa 25 ga watan Yuli, 2025.
Rikicin ya yi sanadin wanda ya hana zana jarabawar darusa 13 da takardu 29.
Hukumar na tattaunawa da gwamnati don sake bai wa ɗaliban damar rubuta jarabawar.
NECO ta kuma bayyana cewa an samu makarantu 38 daga jihohi 13 ds laifin aikatar satar amsa yayin zana jarabawa.
Za a gayyace su zuwa babban ofishin NECO kafin ɗaukar mataki a kansu.
Haka kuma, hukumar ta dakatar da mutum tara da ke aikin sanya ido sake kula da jarabawa saboda gazawarsu wajen hana satar amsa.
Mutanen da aka dakatar, uku sun fito daga Jihar Ribas, uku daga Babban Birnin Tarayya, da kuma mutum ɗai-ɗai daga Jihohin Neja, Kano da Osun.