HausaTv:
2025-07-26@19:25:40 GMT

 Gaza: Ana Ci Gaba Da Samun Shahidai Da Yunwa Take Kashewa A Gaza

Published: 26th, July 2025 GMT

A daidai lokacin da aka cika kwanaki 659 daga fara kisan kiyashin Gaza, sojojin Sahayoniya suna ci gaba da killace yankin da hana shigar da abinci da magani.

Ma’aiktar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa ya zuwa wannan lokacin jumillar wadanda yunwa ta kashe sun kai 122 daga cikinsu da akwai kananan yara 83.

Da jijjifin safiyar yau Asabar, majiyar asibitin “Nasr’ ta sanar da cewa wata jaririya ta yi shahada saboda rashin abinci mai gina jiki. Haka nan kuma ta ce, jaririyar ‘yar watanni 6 da haihuwa ta yi shahada ne saboda rashin abinci mai gina jiki da kuma magani saboda takunkumin da HKI ta kakabawa yankin na Gaza.

Babban jami’iin gudanarwa na ma’aikatar kiwon lafiya a Gaza Dr. Munir al-Bursh ya sanar da cewa; Ana kara samun masu mutuwa saboda yunwa, musamman ma dai a tsakanin kananan yara.

Al-Bursh ya fada wa tashar talabijin din al-jazira cewa; Yunwa saboda rashin abinci da kuma rashin Magani ya sa jariran da suke cikin  mata 3,000 sun mutu.

Haka nan kuma ya nuna mamakinsa akan yadda duniya ta gajiya wajen iya shigar da madarar jarirai cikin yankin Gaza domin ceto da rayuwar kananan yara da jarirai.

A wannan tsakanin ne dai Asusun kananan yara na MDD ( Unicef) ya yi gargadi akan mummunan halin da yaran Gaza suke ci gaba da shiga saboda rashin abinci mai gina jiki.

Ita kuwa shugabar hukumar Agaji ta kasa da kasa “Rd Cross” ta yi kira ne da a kawo karshen wahalhalu da bala’in da aka jefa mutane a Gaza, cikin gaggawa ba tare da ba ta lokaci ba.

A wani labarin na daban, kafafen watsa labarun HKI sun ce, sojojin Sahayoniya sun lalata tarin abinci mai yawa da aka ware domin shigar da shi zuwa yankin Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: saboda rashin abinci kananan yara

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa

Duk da cewa yanayin duniya ya yi babban sauyi, kamata ya yi a mayar da hankali ga hadin gwiwa, yayin da ake raya dangantaka tsakanin Sin da EU, kana bangarorin biyu su bi hanya mafi dacewa, da samun kyakkyawar makoma a shekaru 50 masu zuwa, da kuma kara samar da gudummawa ga dukkanin sassan duniya. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Burtaniya Zata Fara Jefawa Falasdinawa Abinci Daga Sama
  • ‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki
  • ‘Yan Jarida Da Suka yi Shahada A Gaza Sun Kai 232, Yayin Da Wadanda Suka Rasa Rayukansu Sakamakon Yunwa Suka Kai 122
  • Sin Da EU Suna Kokarin Samun Moriyar Juna A Shekaru 50 Masu Zuwa
  • An kashe mata da yara a sabon harin Filato
  • Hukumar Ba Da Agajin Jin Kai Ta ‘Yan Gudun Hijirar Falasdinawa Ta “UNRWA” Ta Sanar Da Kashe Ma’aikatan 330 A Gaza
  • Fiye Da  Falasdinawa 111 Ne Su Ka Yi Shahada Saboda Yunwa A Gaza
  • Asusun Kula Da Kananan Yara Na Majalisar Dinkin Duniya “UNICEF” Ya Yi Gargadi Kan Bala’in Jin Kai A Gaza
  • Gwamantin Kasar Siriya Ta Rufe Hanyoyin Shiga BirninSiweida Na Kasar Saboda Ci Gaba Da Bullar Rikici