Aminiya:
2025-07-26@20:16:38 GMT

Wani mutum ya buɗe Ofishin Jakadancin Indiya na bogi a ƙasar

Published: 26th, July 2025 GMT

’Yan sanda sun kama wani mutum da ya buɗe Ofishin Jakadancin Ƙasar Indiya na bogi wani gidan haya, kuma yake gabatar da kansa a matsayin ambasadan ƙasar.

Jami’an tsaron sun kama mutumin mai suna Harshvardhan Jain ne a ofishin nasa da ke kusa da Delhi, babban birnin ƙasar, kamar yadda Kamfanin Dillancin Labarai na AP ya ruwaito.

Sushil Ghule, Babban Jami’in Rundunar ’Yan Sanda ta Musamman a yankin Uttar Pradesh, ya ce an ƙwace motocin alfarma masu ɗauke da lambar Ofishin Jakadancin Indiya na bogi a hannun mutumin mai shekara 47.

Ya bayyana cewa ambasadan bogin yana damafarar mutane da alƙawuran samun aiki a ƙasashen waje; musamman inda yake iƙirarin zama Jakada ko Mashawarci ga ka kamfanoni irin su “Seborga” ko “Westarctica” da sauransu.

Matashi ya tono gawar kakarsa don yin tsafin kuɗi ya sare kan gawar kakarsa don yin tsafi Ta’addanci: Alƙawuran sojoji 8 na kamo Bello Turji

Ghule ya ce sauran kayan da aka kama Jain da su su haɗa da tambarin Ofishin Jakadancin Indiya da na wasu ƙasashe kimanin 40, duk na bogi.

An kuma kama tsabar kuɗi kimanin Dala dubu 52 (sama da Rupee miliyan 4.5 na Indiya) na kuɗaɗen kasashe daban-daban da aka yi wa ado da tutocin ƙasashen.

Kazalika an kama hotunan Jain da aka yi wa suddabaru aka hada shi da shugabannin duniya.

Ghule ya shaida wa kafar cewa ambasadan bogin yana fuskantar tuhume-tuhume da suka haɗa da zargin safarat kuɗaɗen Haram, yin ungulu da kan zabo, da kuma mallaka da amfani da takardun bogi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Damfara Harshvardhan Jain Indiya Jakadancin Indiya

এছাড়াও পড়ুন:

NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159

Da yake bayar da cikakken bayani kan lamarin, Afolabi ya ce, “Wacce ake zargin, Abigail Brains Timothy, ta yi zargin cewa ta yaudari Fasto Adewusi ta hanyar karyar cewa tana da karfin da alaka da sayen biza da takardun aiki ga mutane 65, wadanda Fasto ya gabatar da ita a matsayin abokan huldarsa.

“A karkashin wannan wakilcin na karya, ta sa shi ya sake mata kudaden da aka ambata na tsawon wani lokaci da nufin biyan kudin biza mai dauke da izinin aiki.

“A ranar 25 ga Mayu, 2025, jami’an NSCDC, reshen Jihar Ekiti, da ke aiki bisa wani korafi da kuma tattara bayanan sirri, sun kama wadda ake zargin a garin Benin bayan da suka yi ta nemanta, bayan ta gudu daga Legas zuwa Benin, Jihar Edo, inda aka bi ta aka kama ta.

“Bayan an kama ta, hukumar NSCDC ta jihar ta gudanar da cikakken bincike daga hukumar leken asiri da bincike ta NSCDC, bincike ya tabbatar da cewa wacce ake zargin ta aikata laifin da gangan kuma ba ta da wata hanya ta gaske ko kuma niyyar cika biza da kuma shirye-shiryen daukar aiki da ta yi alkawari,” in ji shi.

Afolabi ya nanata kudurin hukumar na jihar na kare rayuka da dukiyoyi, duk wasu muhimman kadarorin kasa da kayayyakin more rayuwa da kuma gurfanar da duk wani nau’i na laifukan zagon kasa ga tattalin arzikin kasa kamar hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, fasa bututun mai, da sauran su, a cikin aikin da ya dora mata.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
  • NSCDC Ta Gurfanar Da Wanda Ake Zargi Da Badakalar Naira Miliyan 159
  • Matashi ya tono gawar kakarsa don yin tsafin kuɗi da ƙoƙon kanta
  • Fasakwauri: ‘Yansandan Indiya Sun Kama ‘Yar Nijeriya Da Kwayar Dala Miliyan 4
  • Matashi ya tono gawar kakarsa don yin tsafin kuɗi ya sare kan gawar kakarsa don yin tsafi
  • Wasu Mahara Sun Sake Kashe Mutum 14 A Wani Kauyen Jihar Filato
  • An kama budurwa mai shekara 19 da ake zargi da kashe yara 2 a Bauchi
  • Tinubu ya fi mayar da hankali wajen gina Kudancin Nijeriya — Kwankwaso
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace