Aminiya:
2025-09-18@01:00:14 GMT

Wani mutum ya buɗe Ofishin Jakadancin Indiya na bogi a ƙasar

Published: 26th, July 2025 GMT

’Yan sanda sun kama wani mutum da ya buɗe Ofishin Jakadancin Ƙasar Indiya na bogi wani gidan haya, kuma yake gabatar da kansa a matsayin ambasadan ƙasar.

Jami’an tsaron sun kama mutumin mai suna Harshvardhan Jain ne a ofishin nasa da ke kusa da Delhi, babban birnin ƙasar, kamar yadda Kamfanin Dillancin Labarai na AP ya ruwaito.

Sushil Ghule, Babban Jami’in Rundunar ’Yan Sanda ta Musamman a yankin Uttar Pradesh, ya ce an ƙwace motocin alfarma masu ɗauke da lambar Ofishin Jakadancin Indiya na bogi a hannun mutumin mai shekara 47.

Ya bayyana cewa ambasadan bogin yana damafarar mutane da alƙawuran samun aiki a ƙasashen waje; musamman inda yake iƙirarin zama Jakada ko Mashawarci ga ka kamfanoni irin su “Seborga” ko “Westarctica” da sauransu.

Matashi ya tono gawar kakarsa don yin tsafin kuɗi ya sare kan gawar kakarsa don yin tsafi Ta’addanci: Alƙawuran sojoji 8 na kamo Bello Turji

Ghule ya ce sauran kayan da aka kama Jain da su su haɗa da tambarin Ofishin Jakadancin Indiya da na wasu ƙasashe kimanin 40, duk na bogi.

An kuma kama tsabar kuɗi kimanin Dala dubu 52 (sama da Rupee miliyan 4.5 na Indiya) na kuɗaɗen kasashe daban-daban da aka yi wa ado da tutocin ƙasashen.

Kazalika an kama hotunan Jain da aka yi wa suddabaru aka hada shi da shugabannin duniya.

Ghule ya shaida wa kafar cewa ambasadan bogin yana fuskantar tuhume-tuhume da suka haɗa da zargin safarat kuɗaɗen Haram, yin ungulu da kan zabo, da kuma mallaka da amfani da takardun bogi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Damfara Harshvardhan Jain Indiya Jakadancin Indiya

এছাড়াও পড়ুন:

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
  • DSS ta maka Sowore da Facebook a Kotu kan cin zarafin Tinubu
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin
  • Sarki Sanusi II ya koka kan yawan cin bashin Najeriya