Bisa alkaluman da aka fitar a dandalin shafin intanet, ya zuwa ranar 27 ga watan, jimillar kudin shigar da kasuwar fina-finai ta Sin ta samu a lokacin zafi na bana ya zarce yuan biliyan 5, kuma adadin masu kallon fina-finai a lokacin ya kai miliyan 129.

Bana shekara ce ta cika shekaru 80 da samun nasarar yaki da hare-haren sojojin Japan da kuma yaki da mulkin danniya a duniya ko kuma yakin duniya na biyu.

Daya-bayan-daya zuwa yanzu, ana ci gaba da fitar da wasu fina-finai, da shirye-shirye, da wasannim kwaikwayo, da kide-kide, da raye-raye da kuma ayyukan fasaha dake da jigon tunawa da tarihin yaki da hare-haren na Japan da kuma gadon ruhin yaki da hare-haren.

Daga cikinsu, za a fitar da manyan fina-finai guda uku dake kunshe da “Dakin daukar hoto na Nanjing” nan ba da jimawa ba. Wadannan ayyuka sun dogara ne kan hakikanin abubuwan da suka faru a tarihi, wadanda ke nuna yadda jama’ar kasar Sin suka yaki hare-haren na Japan ta bangarori daban-daban, da kuma nuna babban karfin ruhin yaki da hare-haren. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: yaki da hare haren

এছাড়াও পড়ুন:

HKI Ta ce Ta Tsaida Yaki A Gaza Na Wani Lokaci

Majiyar sojojin HKI ta bada sanarwan cewa sun tsaida yaki na wucin gadi a gaza, don baya kungiyoyin agaji na MDD su shigar da abinci zuwa zirin gaza inda Falasdinawa suke mutuwa saboda yunwa.

Babu wata majiya ta MDD ko kuma na kungiyoyin agaji masu zaman kansu da suka tabbatar da labarin. Kuma mafi yawan kungiyayin sun bayyana cewa sai gani a kasa. Don hki ba abar amincewa bace. Tun shekara ta 2023 ne HKI ta kara tsananta hana shigo da abinci gaza.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana
  • HKI Ta ce Ta Tsaida Yaki A Gaza Na Wani Lokaci
  • Za mu ba da damar shigar da kayan agaji a Gaza — Isra’ila
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Yi Furuci Da Halakar Sojan Guda Da Ya Jikkata A Zirin Gaza
  • Mutane 6 Ne Suka Yi Shahada Sanadiyyar Hare-haren Yan Ta’adda A Zahidan
  • Binciken Jin Raayoyi Na CGTN: Duniya Ta Saba Da “Kauracewar” Amurka
  • ‘Yan Majalisa Sun Zargi Hukumomin Gwamnati Da Wawure Sama Da Naira Biliyan 103.8
  • Yadda aka mayar da yaran da aka sace a Kano masu wanke-wanke a Kudu
  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU