Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5
Published: 27th, July 2025 GMT
Bisa alkaluman da aka fitar a dandalin shafin intanet, ya zuwa ranar 27 ga watan, jimillar kudin shigar da kasuwar fina-finai ta Sin ta samu a lokacin zafi na bana ya zarce yuan biliyan 5, kuma adadin masu kallon fina-finai a lokacin ya kai miliyan 129.
Bana shekara ce ta cika shekaru 80 da samun nasarar yaki da hare-haren sojojin Japan da kuma yaki da mulkin danniya a duniya ko kuma yakin duniya na biyu.
Daga cikinsu, za a fitar da manyan fina-finai guda uku dake kunshe da “Dakin daukar hoto na Nanjing” nan ba da jimawa ba. Wadannan ayyuka sun dogara ne kan hakikanin abubuwan da suka faru a tarihi, wadanda ke nuna yadda jama’ar kasar Sin suka yaki hare-haren na Japan ta bangarori daban-daban, da kuma nuna babban karfin ruhin yaki da hare-haren. (Safiyah Ma)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: yaki da hare haren
এছাড়াও পড়ুন:
Ƙasashe 12 da suka samu tikitin Kofin Nahiyyar Afrika na mata
A ci gaba da wasannin neman shiga gasar cin kofin Nahiyyar Afirka na 2026 da ƙasar Morocco zata karɓi baƙunci, yanzu haka ƙasashe 6 sun samu nasarar shiga gasar.
Ƙasashen da suka samu tikitin sun haɗa da mai masaukin baƙi: Morocco da Najeriya da Zambia da Tanzania da Malawi da Algeria da Ghana da Senegal da Kenya da Burkina Faso da Cape Verde da Afrika ta Kudu.
Gwamnan Bauchi na neman ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi 29 ACF ta mara wa gwamnatin Tinubu bayaWannan dai ita ce gasa karo na 14 da za a buga a tarihi daga ranar 17 ga watan Maris zuwa 3 ga watan Afrilu na 2026.
Ƙasashen da suka kai wasan kusa da na ƙarshe a Kofin Nahiyyar Afirkan za su wakilci nahiyar a Kofin duniya na mata da za a buga a ƙasar Brazil a 2027.