Ana Zaman Dar-dar A Kasar Zimbabwe Saboda Shirin Zanga-zangar Tsofaffin Sojaji
Published: 1st, April 2025 GMT
Jami’an tsaro sun bazama akan titunan manyan garuruwan kasar Zimbabwe domin dakile zanga-zangar da ake shirin yi domin yin kira ga shugaban kasa Emmerson Mnangagwa ya yi murabus.
Tsofaffon sojoji da mayakan da su ka samarwa kasar ‘yanci ne dai suka yi kiran a yi zanga-zangar, saboda kin amincewa da shirin shugaban kasar na tsawaita wa’adin mulkinsa.
A cikin watan Janairu na wannan shekarar ne dai jam’iyyar ZANU-Party, mai mulki a kasar ta sanar da cewa tana son Mnangagwa ya ci gaba da rike mukamin shugaban kasar har zuwa 2023.
Mnangagwa dai ya hau karagar mulkin kasar ta Zimbabwe ne tun a 2017,bayan sauke Robert Mugabe daga kan karagar mulki cikin ruwan sanyi.
Shugaban mayakan nemawa kasar ‘yanci Blessed Geza ya zargi shugaban kasar da cin hanci da rashawa da kuma yi wa kujerar mulki rikon danko.
Shugaban kasar ta Zimbabwe dai ya sha bayyana cewa, ba ya da nufin tsawaita lokacin shugabancinsa.
Kundin tsarin mulkin Zimbabwe wanda aka rubuta a 2013 ya kayyade wa’adin shugabancin kasar na shekaru biyar sau biyu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: shugaban kasar
এছাড়াও পড়ুন:
MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania
Hukumar kare hakkin bil’adam dake karkashin MDD ya sanar da cewa tana sa ido akan kashe-kashe da rashin adalcin da ake yi a karkashin zaben shugaban kas ana kasar Tanzania. Tun a ranar Larabar da ta gabata ne dai da ake zaben rikici ya barke a kasar sabod kin amincewar ‘yan hamayya akan yadda zaben zai gudana ba tare da manyan ‘yan takara ba. Shugabar kasar Samia Suluhu Hassan ce dai babbar ‘yar takara. Babbar jam’iyyar adawa ta sanar da cewa fiye da mutane 700 ne aka kashe a fadin kasar da ake Zanga-zanga. Shugaban ofishin hukumar kare hakkin bil’adama na MDD Seif Magango ya sanar da cewa; Sun karbi rahoranni daga majiya mai tush akan cewa a kalla an kashe mutane 10. Hukumar ta yi kira ga jami’an tsaron kasar ta Tanzania da su daina amfani da karfi a inda bai dace ba, daga cikin har da amfani da makamai akan masu Zanga-zanga. Haka nan kuma sun yi kira ga masu Zanga-zanga da su yi a cikin ruwan sanyi. Ita kuwa kungiyar kare hakkin bil’adama ta “Amnesty International” ta ce nata rahoton ya tabbatar mata da cewa an kashe abinda bai kasa mutane 100 ba. Tuni dai aka kafa dokar ta baci da hana zirga-zarga a babban birnin ksar Darus-salam, ana kuma rufe hanyoyin sadarwa na interten daga lokaci zuwa lokaci. Har ila yau MDD tana yin kira da a saki dukkanin wadanda ake tsare da su.Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada November 1, 2025 Shugaban Kasar Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini November 1, 2025 Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific November 1, 2025 Israila Ta Kai Hari Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A November 1, 2025 Amurka Na Shirin Kai Hari Kan Kasar Venzuwela A Kowanne Lokaci November 1, 2025 Iran Ta Sanya Da Ranar 30 Ga Watan Nuwamba A Matsayin Ranar Kasa Ta Tsibirai 3 October 31, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci