Daruruwan Jama’a Sun Halarci Sallar Jana’izar Marigayi Sarkin Gusau
Published: 26th, July 2025 GMT
Daruruwan mutane daga sassa daban-daban na Jihar Zamfara da wajen ta sun halarci Sallar jana’izar marigayi Sarkin Gusau, Dr. Ibrahim Bello, wanda ya rasu a daren Alhamis bayan gajeruwar rashin lafiya.
An gudanar da Sallar jana’izar ne a Masallacin Jumu’a na Gusau da ke Kanwuri, inda Mataimakin Babban Limamin masallacin, Malam Abdulkareem Umar, ya jagoranci addu’o’in.
172-days_english-3316981
Daga cikin manyan baki da suka halarta har da Gwamnan Jihar Zamfara, Dr. Dauda Lawal, wanda ya bayyana marigayin a matsayin Uba ga kowa, shugaba mai son zaman lafiya, kuma mutum mai hikima wanda ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen ci gaba da hadin kan jihar.
Gwamna Lawal ya nuna alhini matuka game da rasuwar Sarkin, inda ya yi addu’ar Allah ya jikansa ya gafarta masa. Ya kuma bukaci al’ummar jihar da su yi koyi da kyawawan halayen marigayin na tawali’u, adalci da kokarin tabbatar da zaman lafiya.
Haka zalika, mataimakin gwamna, Mani Malam Mummuni, sakataren gwamnatin jihar, manyan jami’an gwamnati, ‘yan majalisar dokoki ta jiha, sarakuna, malamai da daruruwan al’ummar gari daga fannoni daban-daban sun halarci Sallar.
Su ma ‘yan majalisar wakilai da ke wakiltar Maru/Bungudu da kuma Gusau a Majalisar Wakilai ta Tarayya, Dr. Abdulmalik Zannan Bungudu da Kabiru Ahmad Maipalace, sun halarci jana’izar.
Haka kuma dukka sarakunan masu daraja ta farko a Jihar Zamfara da hakimai daban-daban sun halarci sallar jana’izar.
Marigayi Sarkin Gusau, Dr. Ibrahim Bello, wanda ya hau karagar mulki a shekarar 2004, ya shahara fannin ilimi, da kuma kokarin tabbatar da zaman lafiya a Jihar Zamfara.
Rasuwarsa ta zamto babban rashi ga masarautar da ma al’ummar jihar baki ɗaya.
An binne shi a makabartar Kwata da ke Gusau, yayin da ake ci gaba da zuwa ta’aziyya da yi masa addu’a.
Daga Aminu Dalhatu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sarkin Gusau Zamfar sun halarci Sallar Sallar jana izar Jihar Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas
A yau, 17 ga watan Satumba, Shugaba Tinubu ya ɗage dokar ta-ɓaci da ya ƙaƙaba wa al’ummar jihar Ribas biyo bayan rashin jituwa da yaƙi ci yaƙi cinyewa da ya dabaibaye ɓangaren zartarwa da na dokokin jihar. Cikakken bayani na nan tafe…
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp