Daruruwan Jama’a Sun Halarci Sallar Jana’izar Marigayi Sarkin Gusau
Published: 26th, July 2025 GMT
Daruruwan mutane daga sassa daban-daban na Jihar Zamfara da wajen ta sun halarci Sallar jana’izar marigayi Sarkin Gusau, Dr. Ibrahim Bello, wanda ya rasu a daren Alhamis bayan gajeruwar rashin lafiya.
An gudanar da Sallar jana’izar ne a Masallacin Jumu’a na Gusau da ke Kanwuri, inda Mataimakin Babban Limamin masallacin, Malam Abdulkareem Umar, ya jagoranci addu’o’in.
172-days_english-3316981
Daga cikin manyan baki da suka halarta har da Gwamnan Jihar Zamfara, Dr. Dauda Lawal, wanda ya bayyana marigayin a matsayin Uba ga kowa, shugaba mai son zaman lafiya, kuma mutum mai hikima wanda ya bayar da gagarumar gudunmawa wajen ci gaba da hadin kan jihar.
Gwamna Lawal ya nuna alhini matuka game da rasuwar Sarkin, inda ya yi addu’ar Allah ya jikansa ya gafarta masa. Ya kuma bukaci al’ummar jihar da su yi koyi da kyawawan halayen marigayin na tawali’u, adalci da kokarin tabbatar da zaman lafiya.
Haka zalika, mataimakin gwamna, Mani Malam Mummuni, sakataren gwamnatin jihar, manyan jami’an gwamnati, ‘yan majalisar dokoki ta jiha, sarakuna, malamai da daruruwan al’ummar gari daga fannoni daban-daban sun halarci Sallar.
Su ma ‘yan majalisar wakilai da ke wakiltar Maru/Bungudu da kuma Gusau a Majalisar Wakilai ta Tarayya, Dr. Abdulmalik Zannan Bungudu da Kabiru Ahmad Maipalace, sun halarci jana’izar.
Haka kuma dukka sarakunan masu daraja ta farko a Jihar Zamfara da hakimai daban-daban sun halarci sallar jana’izar.
Marigayi Sarkin Gusau, Dr. Ibrahim Bello, wanda ya hau karagar mulki a shekarar 2004, ya shahara fannin ilimi, da kuma kokarin tabbatar da zaman lafiya a Jihar Zamfara.
Rasuwarsa ta zamto babban rashi ga masarautar da ma al’ummar jihar baki ɗaya.
An binne shi a makabartar Kwata da ke Gusau, yayin da ake ci gaba da zuwa ta’aziyya da yi masa addu’a.
Daga Aminu Dalhatu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sarkin Gusau Zamfar sun halarci Sallar Sallar jana izar Jihar Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Jihar Jigawa Na Kara Bullo Da Shirye-shiryen Inganta Rayuwar Masu Bukata Ta Musamman
A kokarin ta na inganta jin dadin al’umma, Gwamnatin jihar Jigawa ta gudanar da aikin tantance masu bukata ta musamman 200 a yankin Karamar Hukumar Birnin Kudu.
A jawabin daya gabatar, shugaban Karamar Hukumar, Dr Builder Muhammad Uba ya godewa gwamnatin jihar bisa kula da jin dadin masu bukata ta musamman a yankin da ma jihar baki daya.
Dr. Builder Muhammad, yace a baya akwai masu bukata ta musamman mutum 61 da ke con gajiyar shirin a yankin amma a yanzu kuma gwamnatin jihar ta amince a kara 139 da za a zabo daga mazabu 11 na yankin.
Builder, wanda ya sami wakilcin Kansila mai kula da shirin walwalar jama’a na yankin, Alhaji Ahmed magaji Bashir, yace Karamar Hukumar za ta bada hadin kai domin samun nasarar shirin a yankin.
A cewar sa, an samu karin alawus na masu bukata ta musamman daga naira dubu 7 zuwa dubu 10.
Shi ma a nasa, jawabin, jami’in shirin na yankin, Mallam Mansir Dahiru yace suna tantance masu bukata ta musamma da suka cancanta domin amfana da shirin a Karamar Hukumar ta Birnin Kudu.
Usman Mohammed Zaria