Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50
Published: 26th, July 2025 GMT
Ya sanar da cewa, manufar aikin ta faro ne, biyo bayan wata ziyarar aiki da Asusun ya ka Jihar Katsina.
“Asusun na NADF, ya dauki kwararan matakai; musamman ta hanyar zuba kudade don yin amfani da Dam din na Sabke da ke Jihar Katsina, domin yin amfani da ruwan da ke cikin Dam, don yin noma na zamani“, in ji Mohammed.
“OCP na Afirka, na da kwararru wadanda tuni suka auna yanayin kadadar da a gudanar da aikin, musamman duba da cewa; za a iya yin amfani da ruwan Dam din na Sabke, wajen gudanar da aikin”, a cewarsa.
Ya kara da cewa, Bankin shi kuma zai samar da wadatattun kudaden da za a yi aikin, wanda kuma Asusun na NADF zai kasance mai sanya ido kan aikin.
Ya kuma bayyana gamsuwar cewa, aikin zai kasance na zamani.
Shi kuwa a nasa jawabin, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda ya sanar da cewa; gwamnatinsa za ta bai wa aikin goyon bayan da ya dace.
“A lokacin da aka gabatar min da batun wannan aiki, nan da nan na aminta da shi, duba da irin dimbin alfanun da ke tattare da aikin, musamman wajen kara bunkasa tattalin arzikin Jihar Katsina da kuma rayuwar ‘yan jihar baki-daya“, in Radda.
“Burinmu shi ne, muga ana yin noma har zuwa gazayowar wata daminar a jihar, musamman domin al’ummarmu su kasance cikin shiri wajen gudanar da ayyuka a koda-yaushe tare kuma da amfana daga kudaden da aka kashe wajen sake gyaran wannan Dam da aka yi watsi da shi a baya”, a cewar gwamnan.
Shi kuwa a nasa bangaren, wakilin OCP na Afirka; Alik Orebaoghene ya sanar da cewa; gonar za ta kasance wajen bayar da horon sanin makamar aikin noma, musamman a tsakanin kananan manoma da ke jihar.
A karkashin wannan hadaka, ana sa ran OCP na Afirka zai samar da ingantaccen takin zamanin da za a gudanar da wannan aiki.
Shi ma, Manajan Daraktan Hukumar SRRBDA; Abubakar Malam, a nasa jawabin, jinjina ya yi kan kokarin da aka yi na sake farfado da wannan aiki.
Ya sanar da cewa, bisa tsarin kudurin Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu (Renewed Hope Agenda), muna alfahari da samar da hektar noma daidai har guda 50, domin aiwatar da wannan aiki; musamman domin kara samar da wadataccen abinci a wannan kasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Ya sanar da cewa ya sanar da cewa Jihar Katsina wannan aiki
এছাড়াও পড়ুন:
Asusun Kula Da Kananan Yara Na Majalisar Dinkin Duniya “UNICEF” Ya Yi Gargadi Kan Bala’in Jin Kai A Gaza
Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya ya yi gargadi karuwar bala’i na jin kai a Gaza
Kazem Abu Khalaf, kakakin hukumar UNICEF a Falasdinu, ya tabbatar da cewa: Abin da ke faruwa a Gaza ba a taba ganin irinsa ba, yana mai cewa har yanzu yana ci gaba da tuntubar wasu ma’aikatan jin kai da dama da suka yi balaguro zuwa yankunan da ake fama da rikici, da bala’o’i, da wuraren yaki a duniya, kuma dukkansu, ba tare da togiya ba, sun amince cewa, ba su taba ganin wani yanayi mai kama da abin da ke faruwa a Gaza ba.
Abu Khalaf ya yi nuni da cewa: Mutanen yankin Zirin Gaza sun fara fama da yunwa, sannan kuma kishirwa, gami da fuskantar kisa, yayin da aka jibge kayan agajin jin kai a kan iyakar da ke da tazarar kilomita goma kacal. Motar bas guda na iya daukar sa’a guda-ko kuma akalla sa’a daya da rabi kafin ta isa tsakiyar zirin Gaza da agaji, amma sojojin mamayar Isra’ila ba za su kyale ta.
Ya bayyana cewa, kasashen duniya suna nuna halin ko-in-kula, tare da nuna rashin damuwa da daukan abin da muhimmanci daga Larabawa a hukumance da kuma juya baya daga al’ummar Larabawan.