Aminiya:
2025-07-25@21:33:43 GMT

Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan kisan sama da mutum 100

Published: 24th, July 2025 GMT

Wasu mazauna Ƙaramar Hukumar Gusau da ke Jihar Zamfara, sun yi zanga-zangar lumana tare da neman gwamnati ta ɗauki kan ƙaruwar hare-haren ’yan bindiga a yankin.

Zanga-zangar ta fara ne da misalin ƙarfe 12 na ranar Laraba.

Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na ƙasa Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid a Borno

Jama’a da dama sun halarci zanga-zangar; wasu a kan babura, wasu a cikin motoci, wasu kuma a ƙafa.

Kuma sun taru a ƙofar gidan gwamnatin Jihar da ke Gusau domin nuna damuwarsu.

Ƙauyukan da abin ya fi shafa sun haɗa da Mada, Ruwan Bore, Fegin Baza, Bangi, Lilo, Wonaka, da Fegin Mahe.

Mazauna yankunan sun ce sama da mutum 100 ’yan bindiga suka kashe a baya-bayan nan.

Wani daga cikin masu zanga-zangar, Malam Abubakar Abdullahi daga ƙauyen Fegin Mahe, ya ce ’yan bindiga sun kashe ’yan uwansa da dama, sannan kuma sun sace musu kaya da darajarsu ta haura Naira miliyan ɗaya, ciki har da buhun taki guda 500.

Hare-haren sun hana manoma yin aiki a gonakinsu, saboda rashin tsaro a yankin.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Gusau, Abubakar Iman, ta bakin wakilinsa Aminu Wakili Mada, ya ce ya fahimci ƙorafin jama’ar yankunan.

Ya tabbatar da cewa gwamnati tare da jami’an tsaro suna aiki tare domin tabbatar da zaman lafiya, kuma za a tura ƙarin jami’an tsaro zuwa wuraren da suka fi fama da matsala nan ba da jimawa ba.

Yunƙurin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Yazid Abubakar, ya ci tura domin bai amsa waya ba.

A wani labarin kuma, jami’an tsaro sun ceto mutum 11 da aka sace a dajin da ke Ƙaramar Hukumar Zurmi a Jihar Zamfara.

An sace mutanen ne a ƙauyen Kaibaba da ke gundumar Turba a Ƙaramar Hukumar Isa a Jihar Sakkwato.

An miƙa su ga Gwamnatin Jihar Sakkwato a ranar Laraba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gwamnati hari Neman Ɗauki Zamfara Ƙaramar Hukumar zanga zangar

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Da Karamar Hukumar Dutse Za Su Shirya Taron Bita Ga Kansiloli

Shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar Dokokin jihar Jigawa, Alhaji Aminu Zakari, ya bayyana cewa gudanar da ayyukan raya kasa sosai a yankunan karkara zai kara daga martabar jihar a idon sauran jihohin kasar nan.

Ya yi wannan tsokaci ne yayin ziyarar aiki a sakatariyar karamar hukumar Dutse, inda ya ja hankalin shugaban karamar hukumar game da bukatar bada fifiko ga bangaren ayyukan raya kasa fiye da harkokin yau da kullum domin karfafa matakin cigaban karamar hukumar.

A cewar sa, kwamatin na rangadin kananan hukumomin jihar 27 ne domin bibiyar yadda ake aiwatar da tanade tanaden kasafin kudi domin tabbatar da kashe kudaden gwamnati ta hanyar da ta dace, Inda Kwamatin ke duba kundin bayanan sha’anin mulki da na harkokin Kudi da nufin cusa dabi’ar aiki da tanade tanaden aikin gwamnatin da ka’idojin kashe kudade.

Kazalika, Alhaji Aminu Zakari yace an kafa kananan kwamitoci guda 2 domin ziyarar gani da ido kan ayyukan raya kasa da karamar hukumar Dutse ta gudanar ga jama’ar yankin.

Karamin Kwamati na daya bisa jagorancin wakilin mazabar
Kanya Babba Alhaji Ibrahim Hashim Kanya, ya duba aikin ginin Masallacin khamsissalawati na garin Barangu da rumfunan kasuwa a garin ‘Yar Gaba da Masallacin khamsissalawati na Gidan Gawo da aikin ginin karamin asibitin garin Charka da aikin karamin asibitin Zangon Buji, da aikin gyaran Masallacin Juma’a na garuruwan Kacha da Barandau.

Shi kuwa karamin kwamati na 2 bisa jagorancin wakilin mazabar Buji, Alhaji Sale Baba Buji ya duba aikin hanyar Burji daga Bolari ta wuce Bakin Jeji zuwa Katangar lafiya, akan naira milyan 129 wadda wani kamfani ya yi, sai kuma rumfar kasuwa a garin Hammayayi da sanya fitilu masu amfani da hasken rana makaranta sikandire ta garin Madobi da Masallacin Juma’a na garin Baranda.

A jawabin sa na maraba, shugaban karamar hukumar Dutse Malam Sibu Abdullahi, ya bayyana ayyukan Kwamatin a matsayin ginshikin samun nasarar gudanar da mulkin kananan hukumomi.

Ya bayyana kudurin sa na karbar gyare-gyare da shawarwarin Kwamatin domin cigaban karamar hukumar sa.

Malam Sibu Abdullahi ya bayyana kudurinsa na hada Kai da majalisar Dokokin jihar Jigawa domin shiryawa kansiloli da Akawun majalisar kamsilolin bita game da tsare tsaren zaman majalisa kamar yadda mataimakin sakataren Kwamatin Malam Sadiq Muhammad ya kawo shawara.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun ceto yaro da aka sayar shekaru 3 a Filato
  • An yanke wa mutum 3 hukuncin kisa kan kisan kai a Gombe
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Da Karamar Hukumar Dutse Za Su Shirya Taron Bita Ga Kansiloli
  • Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja
  • Ɓullar Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja
  • Ruwa da iska sun kashe mutum 5, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Ruwa da iska sun kashe mutum, sun raba sama da 5,000 da muhallansu a Yobe
  • Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan kisan mutum sama da 100
  • Al’ummar Fegin Mahe Sun Yi Zanga-zanga Kan Kisan Jama’a Da ‘Yan Bindiga Ke Yi