Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya ya yi gargadi karuwar bala’i na jin kai a Gaza

Kazem Abu Khalaf, kakakin hukumar UNICEF a Falasdinu, ya tabbatar da cewa: Abin da ke faruwa a Gaza ba a taba ganin irinsa ba, yana mai cewa har yanzu yana ci gaba da tuntubar wasu ma’aikatan jin kai da dama da suka yi balaguro zuwa yankunan da ake fama da rikici, da bala’o’i, da wuraren yaki a duniya, kuma dukkansu, ba tare da togiya ba, sun amince cewa, ba su taba ganin wani yanayi mai kama da abin da ke faruwa a Gaza ba.

Abu Khalaf ya yi nuni da cewa: Mutanen yankin Zirin Gaza sun fara fama da yunwa, sannan kuma kishirwa, gami da fuskantar kisa, yayin da aka jibge kayan agajin jin kai a kan iyakar da ke da tazarar kilomita goma kacal. Motar bas guda na iya daukar sa’a guda-ko kuma akalla sa’a daya da rabi kafin ta isa tsakiyar zirin Gaza da agaji, amma sojojin mamayar Isra’ila ba za su kyale ta.

Ya bayyana cewa, kasashen duniya suna nuna halin ko-in-kula, tare da nuna rashin damuwa da daukan abin da muhimmanci daga Larabawa a hukumance da kuma juya baya daga al’ummar Larabawan.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya

Imam Ali shi ne halifan Annabi Muhammad na hudu a mahangar Ahlussunnan, amma mabiya mazhabar Shi’a na daukar sa a matsayin na farko daga cikin imamansu 12.

Wannan ya sanya akasarin mabiya Shi’a na Iraki kan bukaci a binne su a makabartar, kuma sanadiyyar saukin sufuri a zamunnan baya-bayan nan, wasu mabiya Shi’a daga kasashen duniya kan so a binne su a makabartar.

Tsarin makabartar ya kasance cakuduwa ce ta gine-ginen hubbarai irin na zamanin baya, da hanyoyi masu tsuku da suka ratsa ta cikinta da kuma wasu wurare da ake yi wa kallon masu tsarki.

 

Me ya sa ake kiran makabartar Wadi al-Salam?

Ana kiran makabartar da sunan Wadi al-Salam, wato ‘kwarin aminci’ ne saboda dalilai na tarihi da dama.

Dalilai na addini: Ana yi wa makabartar daukar mai daraja, tare da imanin cewa wadanda ke kwance a cikinta na cikin rahama.

Alaka da Imam Ali: Makabartar tana makwaftaka da kabarin Imam Ali bin Abi Talib a birnin Najaf, wanda hakan ya sa Musulmai, musamman mabiya akidar Shi’a ke girmama ta kuma suke kwadayin ganin an binne su a cikinta.

Girma: Makabartar ta kasance mafi girma a duniya, inda ta mamaye wuri mai girman gaske, kunshe da miliyoyin kaburbura, inda ta zamo tamakar wani birni na mamata.

Ziyara: Masu ziyara zuwa birnin Najaf, mai tsarki ga mabiya akidar Shi’a sukan bi ta cikin makabartar tare da karanta Fatiha da kuma yin addu’o’in samun rahama ga wadanda ke kwance, lamarin da ya mayar da wurin tamkar wuri na ziyarar ibada.

Wadannan dalilai ne suka sanya tuntuni aka yi wa wurin lakabi da ‘kwarin aminci’ tun asali, kuma ake ci gaba da kiranta da hakan har yanzu.

 

Tarihin kafuwar makabartar Wadi al-Salam

Makabartar ta samo asali ne tun kafin zuwan addinin Musulunci a lokacin Annabi Muhammad, inda tun kafin wancan lokaci ake binne mutane a wurin.

Wuri ne mai muhimmanci wanda ke karbar bakuncin masu bincike na kimiyya da masana addini, musamman mabiya Shi’a daga sassa daban-daban na duniya.

Wadi al-Salam na da kofofi da dama da ake bi wajen shigar ta, inda hakan ke saukake zirga-zirga ga masu ziyara, kuma yawancin wadannan kofofi na karuwa ne bisa fadadar makabartar.

A shekara ta 2016 ne Hukumar kula da ilimi da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya ta ayyana makabartar a matsayin daya daga cikin wuraren tarihi na duniya.

 

Kalubalen da makabartar ke fuskanta

Daya daga cikin manyan kalubalen da makabartar ke fuskanta shi ne karuwar mutane da ake binnewa a lokacin yaki.

Misali, a lokacin da aka yi fama da rikicin kungiyar ISIS a Iraki, yawan mutanen da ake binnewa a kowace rana a makabartar ya daga zuwa 150 ko 200 a kowace rana, daga gawa 80 zuwa 120 da aka saba.

Wannan ya sanya wuraren binne sabbin mamata ya yi karanci.

 

Farashin binne mamaci

Farashin binne mamaci a makabartar Wadi al-Salam ya danganta ne da lokaci da kuma halin da ake ciki na zaman lafiya.

Ya zuwa farkon shekara ta 2025, kudin sayen filin binne mamaci mai girman murabba’in mita 25 ya kai miliyan biyar na kudn kasar Iraki, wato kimanin Dala 4,100, inda hakan ya nunka farashin da ake biya a lokutan da ake zaman lumana sosai.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025 Manyan Labarai An Kashe Mutum 3 Yayin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Hari Kan Iyakokin Kano November 2, 2025 Manyan Labarai Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima November 1, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya
  • An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya
  • Majalisar Dinkin Duniya ta damu da hare-haren Amurka a Caribbean da Pacific
  • Sanata Sunday Marshall Katung Ya Sauya Sheka Zuwa Jam’iyyar APC
  • Israila Ta Kai Hari  Kan Ofishin kungiyar UNICEF Dake Gaza A
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • M D Duniya Tayi Gargadi Game Da Gwajin Nukiliya Da Amurka Ta Sanar Za ta yi
  • Ranar Foliyo Ta Duniya: Muna Fatan Ganin Karshen Cutar Foliyo A Jihar Katsina -Zulaihat Dikko Radda