NAFDAC ta gano dakin ajiye kayayyaki makare da sinadaran hada bam a Kano
Published: 24th, July 2025 GMT
Hukumar da ke Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Kasa (NAFDAC) a ranar Laraba ta ce ta gano wani dakin ajiye kayayyaki da aka makare da lita 88,560 na sinadaran hada bama-bamai a Kano.
Shugabar hukumar, Farfesa Mojisola Adeyeye ce ta bayyana hakan lokacin da take yi wa manema labarai jawabi a kofar rumbun da ke unguwar Kwakwaci a karamar hukumar Fagge da ke jihar.
Mojisola, wacce Daraktan Bincike da Tabbatar da Bin Doka na hukumar, Dokta Martins Iluyumade ya wakilta, ta ce dakin na dauke ne da lita 60,000 na sinadarin sulphuric acid, sai kuma lita 28,560 na nitric acid da kuma wasu jarkoki 330 da aka riga aka rabar wa mutanen da ba a san ko su wane ne ba, sinadaran cikin su.
NAJERIYA A YAU: Cututtukan da rumar daki ke haifarwa ga jikin mutum Tinubu ya sake miƙa buƙatar karɓo bashin Dala miliyan 347 daga ƙetare“Abin da muka gano yau a nan ya tayar mana da hankali matuka, ba na tunanin a rayuwata na taba ganin adadin irin wadannan sinadaran a waje daya,” in ji shugabar.
Ta ce jami’an hukumar ne tun da farko suka gano wajen, kuma ko da aka je, manajan da ke kula da wajen kawai aka tarar sai wani ma’aikacin wurin, inda aka kama su.
Ta kuma ce, “Ba mu da bayanan mamallakin wajen a matsayin dillalin wadannan sinadaran da gwamnati ta san da zamansa. Mukan ajiye bayanan dukkan masu wannan harkar domin mu rika sa ido a kan shige da fice da kuma amfani da wadannan sinadaran.
“Wadannan sinadaran suna da matukar hatsarin da bai kamata a ce kowa kawai na ta’ammali da su ba. A ka’ida dole sai mutum ya sami izini daga Ofishin mai ba Shugaban Kasa Shawara Kan Harkar Tsaro kafin ya fara shigo da su da kuma izinin mallakarsu, wanda babu daya daga cikin wadannan da mamallakin wurin yake da shi.
“Ana bukatar izinin ne saboda ana iya amfani da sinadaran wajen hada bama-bamai.
“Adadin sinadaran da muka gano a nan sun isa su tashi Kano gaba daya idan aka yi wasa da su,” in ji Mojisola.
Shugabar ta kuma ce yanzu haka suna ci gaba da titsiye mutanen da suka kama domin ganin an kama ainihin mamalakin wajen da ya riga ya cika wandonsa da iska don ya yi musu bayanin su wa yake sayar wa da sinadaran.
Sai dai ta ce za a bi hanyar da ta dace wajen lalata sinadaran bisa bin ka’idojin kiyaye lafiyar al’umma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: wadannan sinadaran
এছাড়াও পড়ুন:
Trump ya fitar da Amurka daga UNESCO saboda amincewa da Falasdinu a matsayin Mamba
Amurka ta yanke shawarar ficewa daga hukumar kula da ilimi da kimiya da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya UNESCO a karo na biyu saboda matakin da ta dauka na shigar da Falasdinu a matsayin mamba.
Mataimakiyar sakatariyar yada labaran fadar White House Anna Kelly ta sanar da matakin a cikin wata sanarwa a ranar Talata.
Kelly ta ce dalilin da ya suka dauki wannan kan hukumar UNESCO, shi ne ta tallafa wa shirye-shiryen da Amurka ke kallonsu a matsayin wadanda ba su dace da muradunta ba.
“Shugaba Trump ya yanke shawarar janye Amurka daga UNESCO, wadda ke kula da ayyuka a bangaren raya al’adu da ilimi da zamantakewar al’umma, saboda daukar wau matakai wadanda ba su dace da manufofin Amurka ba,” in ji Kelly.
Ta ci gaba da cewa, shigar da Falasdinu a matsayin mamba a hukumar UNESCO, Amurka na Kallon hakan a matsayin babbar matsala kuma ya saba wa manufofin Amurka, wanda hakan ke ke kara haifar da karuwar kalaman kyama ga Isra’ila a cikin kungiyar.
Darakta-janar na UNESCO, Audrey Azoulay, ya bayyana matukar Rashin jin dadinsa kan matakin da Trump ya dauka na ficewa daga kungiyar, amma ya kara da cewa dama tuni aka yi hasashen haka, kuma UNESCO ta shirya ma hakan, tare da yin nuni da cewa hukumar ta dauki matakin karkata hanyoyin samar da kudadenta, inda kusan kashi 8% na kasafin kudin ta ke fiowa daga Washington.