Rashin abinci mai gina jiki ya kashe yara 650 a Katsina — MSF
Published: 27th, July 2025 GMT
Wani rahoto daga ƙungiyar likitocin ƙasa da ƙasa wato Medecins Sans Frontiere na nuni da cewa sama da yara 650 ne suka mutu bayan fuskantar ƙarancin abinci mai gina jiki a Jihar Katsina.
Medicins Sans Frontiere wadda ta fara aiki a Katsina tun shekarar 2021, ta ce ta samu ƙaruwar yara masu fama da yunwa sanadiyyar rashin abinci mai gina jiki da aka isar da su zuwa cibiyoyin kula da marasa lafiya da ƙungiyar ke da su a yankin.
A cewarta, a tsakanin Janairu da Yuni 2025 ta yi jinyar kusan yara 70,000 da ke fama da tamowa a Jihar Katsina, ciki har da kusan 10,000 da ke bukatar kulawa da ta dace daga likitoci .
“A wannan shekarar ta 2025 a cewar ƙungiyar, yara 652 suka mutu saboda rashin samun kulawa akan lokaci,” in ji Ahmed Aldikhari, mai magana da suna ƙungiyar ta MSF a Nijeriya, kamar yada sanarwa ta tabbatar a ranar Juma’a.
MSF ta ce yaran da iyaye sun fuskanci tarin matsaloli ne sakamakon raguwar tallafin da ake samu daga ƙasashen duniya, inda manyan ƙasashe masu bayar da tallafi da suka hada da Amurka da Birtania da kuma Tarayyar Turai suka rage kudaden da suke bayarwa.
Ana iya tuna cewa a wannan makon nan da muke bankwana da shi ne Hukumar Samar da Abinci ta Duniya (WFP) ta sanar da dakatar da tallafin abinci na gaggawa ga mutane milyan 1.3 a yankin Arewa maso Gabashin Najeriya daga karshen watan Yuli, sakamakon karancin kudade.
Ƙungiyar ta ce adadin yaran da ke fama da matsalar rashin abinci mai gina jiki wanda ya fi kamari kuma mai barazana ga rayuwa a Jihar Katsina ya karu da fiye da kashi 200 cikin 100 idan aka kwatanta da makamancin lokacin bara.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jihar Katsina tamowa yunwa
এছাড়াও পড়ুন:
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya ce alkaluman baya bayan nan da aka fitar cikin Mujallar Economist, sun shaida yadda hada-hadar cinikayyar fitar da hajoji ta kasar Sin ke kara bunkasa cikin sauri a shekarar nan ta bana, inda fannin ke samun karuwar abokan hulda, da daidaiton matsayi cikin tsarin samar da hajojin masana’antu na kasa da kasa.
Kakakin ya kara da cewa, kasashen duniya suna maraba da hajojin kasar Sin, kuma yakin ciniki da haraji ba su yi wani babban tasiri kan kasar Sin ba. A fannin hada-hadar cinikayya, sanya shinge ba alama ce ta karfin gwiwa ba, kuma katangar da Amurka ke ginawa kanta, daga karshe za ta illata karfinta ne.
Lin Jian, wanda ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da aka saba gudanarwa a yau Laraba, ya ce yayin da ake fama da yanayi mai sarkakiya, da sauye-sauye masu maimaituwa daga ketare, cinikayyar waje ta Sin na gudana lami lafiya, cike da karfin juriya da babban karsashi.
Hakan a cewarsa, ya shaida gazawar yakin haraji da cinikayya wajen girgiza fifikon da Sin ke da shi, a fannin raya masana’antun sarrafa hajoji da kasar ta gina a tsawon lokaci. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp