Masu karatu za su so jin dan takaitaccen tarihinki?

An haife ni a garin Gombe, amma sai daga bisani na bar garin Gomben da zama na dawo Kano, tun ina ‘yar shekara biyar da haihuwa, sakamakon mahaifina yana aiki a Kanon. Kazalika, na girma a gaban iyayena, na yi firamare da sakandare duk a garin Kano, sannan kuma ban taba yin aure ba; budurwa ce ni.

 

Wace irin rawa kike takawa a cikin masana’antar shirya finafinai ta Kannywood?

Ina fitowa ne a matsayin Jaruma kawai, amma kuma ina da niyyar zama mai bayar da umarni a nan gaba kadan insha Allah.

 

Me ya ja hankalinki, har kika tsunduma harkar fim?

Wato batu na gaskiya, fim yana burge ni kwarai da gaske, amma dalilin shigata sana’ar ita ce; wani fim aka yi sai wata arniyya ta musulunta, daga nan ne na ce; in dai har fim yana isar da sako, har ya zama silar gyaruwar al’umma, gaskiya zan zama daya daga cikin wadanda za su isar da wannan sako, tunda da ma raina yana so matuka gaya.

 

Ya gwagwarmayar shiga masana’antar ta kasance?

Gaskiya ni ban sha wahala ba, dalili kuwa shi ne; dan fim ne ya sa ni a harkar ta fim, sannan kuma kamar yaya yake a wajena, dan Unguwarmu ne, iyayena da nasa sun zama kamar ‘yan’uwa.

 

Lokacin da kika fara sanar wa iyayenki cewa, kina son shiga harkar fim, wane kalubale da kika fuskanta daga wurinsu? 

Eh! Gaskiya na fuskanci kalubale, amma daga baya sun fahimce ni, sakamakon iyayen nawa masu fahimta ne.

 

Za ki yi kamar shekara nawa da fara fim?

Ina ga zan samu kamar shekara takwas da farawa.

 

Ya farkon fara dora miki Kyamara ya kasance?

Ban ji tsoron komai ba, kuma Alhamdulillahi na samu yabo sosai daga wajen masu bayar da umarni da sauran abokan aiki.

 

Wane fim kika fara yi a farkon zuwanki?

Na fara ne da fim din Dadin Kowa.

 

Wace rawa kika taka a cikin shirin na Dadin Kowa?

Na fito ne matsayin Sailuba, inda na taka rawa a matsayin matar aure. Surukata ce ta auro wa mijina ni a kauye, saboda ba ta son matar dan nata da aura, sakamakon cewa; Beyerabiya ce, wato maman Rasaki kenan, ni kuma a nan na yi ta tsula tsiyata.

 

Bayan da aka fara haska fuskarki cikin shirin Dadin Kowa, ya kika ji a lokacin, sannan kuma yaya kika kasance da mutanen Unguwarku da sauran ‘yan’uwa?

Alhamdulillah! Wadanda suka san ni a gaske, sun biyo ni har gida suna kallona kamar a da ba su san ni ba, wadanda kuma ba su san ni ba, idan muka hadu abin ba dama, ga tarin alhairai daga masoya daga gurare daban-daban.

 

Bayan shirin Dadin Kowa da kika fito a ciki, ko akwai wasu fina-finan da kika fito ciki?

Eh, na yi wasu fina-finan da dama.

 

Kamar wadanne kenan?

Kamar irin su: Ni da Mijin Yayata, Matar Waye, Zaman Tare, Matar Kaddara da dai sauransu, dukkanninsu masu masu dogon zango ne kuma ni ce jarumar ciki.

 

Cikin wadannan fina-finai da kika zayyano, wane fim ne ya fi burge ki, kuma me yasa, sannan wace rawa kika taka a cikin shirin?

Ni da mijin Yayata, na fito ne a matsayin budurwa wacce take matukar son mijin yayarta.

 

Ya kika ji a lokacin da za ki taka rawa a wannan shirin?

Na ji dadi sosai, saboda zan yi abin da nake so; sannan kuma an kara min kwarin gwiwa, har muka yi muka gama babu wata matsala.

 

Ya batun masu kallo bayan shirin ya fita, ko kin samu wani kalubale daga gare su?

A a, kawai dai idan aka gan ni a zahiri, a kan yi mamaki tare da bayyana cewa; na fi kyau a fili, wasu ma har su ce ba su yi zaton cewa; ‘yar birni ba ce ni, sun yi zaton yadda nake ‘yar kauye a Dadin Kowa, a gaske ma haka nake.

 

A fina-finan da kika yi, wane fim ne ya fi haska ki; har mutane suke iya gane ki?

Dadin Kowa, sai kuma wannan fim din na Matar Waye, shi ma ba abin da zan ce gaskiya.

 

Ko akwai wani kalubale da kika taba fuskanta, tun daga farkon zuwanki cikin masana’antar zuwa yanzu?

Gaskiya an samu, amma a da ne; yanzu cikin ikon Allah an samu daidaito.

 

Wadane irin nasarori kika samu game da fim?

Akwai nasarori da dama kamar ta fuskar samun kudi, mota, kayan sakawa, turaruka da sauran makamantansu.

 

Ko kina da ubangida a masana’antar Kannywood?

Kwarai da gaske ina da su, akwai Adam Musa Adam da kuma Usman Adam Hali Dubu.

 

Kafin ki fara fim, wadane jarumai ne suka fi burge ki har kike jin dama ki zama tamkar su?

Ina kowace jaruma, domin kuwa dukkaninsu suna burge ni.

 

Yaushe kike sa ran yin aure?

Duk lokacin da Allah ya kawo shi, a shirye nake.

 

Ko akwai wanda ya taba cewa yana son ki zai aure ki a masana’antar?

Kwarai da gaske, akwai.

 

Ko za mu iya jin sunansa?

A’a gaskiya.

 

Mene ne ra’ayinki game da auren dan fim?

Zan iya aurensa mana, ai babu wata matsala a ciki.

 

Wane irin namiji kike so ki aura?

Ya kasance Musulmi, mai ilimi, wanda kuma yake da cikakkiyar sana’a.

 

Wace shawara za ki bai wa abokan aikinki na masana’antar Kannywood?

Da farko dai, ya kamata mu hada kanmu, sannan mu kiyaye abin da zai bata sunan sana’ar tamu, mu kuma yi kokari wajen kare mutuncinmu, wannan shi ne a takaice.

 

Wacce shawara za ki bawa masu kokarin shigowa wannan masana’anta?

Su tabbata sun shigo da niyya mai kyau, sannan kuma su yarda cewa; sana’a suka zo yi, ba wani abu daban ba.

 

Ko kina da wadanda za ki gaisar?

Ina fatan alhairi ga kowa da kowa, musamman masoyana.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: a masana antar

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato

Gwamnan Sakkwato, Dakta Ahmad Aliyu, ya ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani guda 20, tare da riguna ruwa (life jackets) 2,000, domin rage haɗurran da ke aukuwa sakamakon ambaliya da nutsewar jirage a sassan jihar.

An ƙaddamar da jiragen ne a ƙaramar hukumar Wamakko a ranar Laraba, inda gwamnan ya bayyana cewa wannan mataki na daga cikin shirin gaggawa na tallafa wa al’ummar da ke fama da illar ambaliya da haɗurra a ruwa.

Microsoft ya ƙwace shafukan wasu kamfanoni 340 a Najeriya An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB

“Mun dauki wannan mataki bayan rahotannin da muke samu na yawaitar hatsarurruka da rasa rayuka da dukiya sakamakon jiragen katako da mutane ke amfani da su,” in ji Gwamna Ahmad Aliyu.

Gwamnan ya miƙa godiya ga shugabar hukumar bayar da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA), Hajiya Zubaida Umar, bisa hadin kai da goyon bayan da hukumar ke bayarwa domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiya, tare da inganta ayyukan ceto da agaji a jihar.

Aminiya ta ruwaito cewa, an horar da direbobin jiragen ruwan da za su riƙa kula da su, kafin a raba su zuwa ƙananan hukumomi goma (10) da suka fi fuskantar barazanar ambaliya da suka haɗa da: Goronyo, Shagari, Sabon-Birni, Wurno, Rabah, Wamakko, Silame, Kebbe, Tambuwal da Isa.

Gwamnan ya kuma yi gargaɗin cewa za a hukunta duk wani da ya ɗauki lodi fiye da ƙima a cikin jiragen, yana mai cewa “wannan jirage da rigar ruwa na jama’a ne, kuma wajibi ne shugabannin ƙananan hukumomi su tabbatar da kula da su yadda ya kamata.”

Sai dai wasu daga cikin mazauna yankunan da za a rabawa jiragen sun bayyana ra’ayinsu dangane da lamarin, inda wani Tanimu Goronyo, daga karamar hukumar Goronyo, ya ce: “Gwamnatin Sakkwato ta kauce hanya.

“Abin da muke bukata a yanzu shi ne hanyoyin mota da magudanan ruwa. Ambaliya tana mamaye yankunan mu ne saboda babu hanya. Idan gwamnati ta kashe wannan kuɗi wajen gina hanya, sai an fi cin moriya.”

Shi ma wani Muhammad Kabiru, daga Silame, ya bayyana farin cikinsa da sayen jiragen, sai dai ya roƙi gwamnati da ta mai da hankali wajen gina hanyoyin mota saboda abin da suka fi buƙata ke nan.

“Mu a Silame jirgi yana da amfani, amma hanyar mota ita ce babbar buƙatar mu. Idan aka samar da ita, ambaliya ba za ta hana mu zirga-zirga ba.”

Yayin da gwamnatin Sakkwato ke ɗaukar matakan gaggawa don rage hatsarurruka da ambaliya ke haifarwa, al’umma na ci gaba da neman tsarin da zai magance tushen matsalar – musamman samar da ingantattun hanyoyi da magudanan ruwa a karkara.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwara ETF Ya Dauki Nauyin Karatun Fitattun Dalibai A Matakin Sakandare
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • ’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote
  • Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
  • Majalisar Dattawa Ce Kawai Za Ta Iya Dawo Da Sanata Natasha – Magatakardar Majalisa
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Fasinjoji 17 A Zamfara