Hajjin Bana: Maniyata 3, 155 Suka Yi Rijista a Kano
Published: 21st, March 2025 GMT
Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano ta ce ta samu nasarar kammala rijistar maniyyata aikin hajjin bana 3,155.
Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Lamin Danbappa, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis a Kano a lokacin da ya karbi bakuncin tawagar gudanarwar Hukumar Shige da Fice a ofishinsa.
Danbappa ya bayyana cewa hukumar ta kammala dukkan shirye-shirye da suka hada da kwasa-kwasan horas da aikin hajji, da takardu da kuma tattara kayanai.
“Yanzu haka hukumar ta fara bayar da biza ga maniyyatan da suka yi rijista.
Ya yabawa gwamnatin jiha bisa yadda take ci gaba da tallafawa kokarin hukumar na ganin an gudanar da aikin Hajji cikin sauki.
A nata bangaren, sabuwar shugabar hukumar shige-da-fice mai kula da filin jirgin sama na Malam Aminu Kano (MAKIA), Aisha Nda ta ce sun kasance a hukumar ne domin bayar da lambar yabo ga Darakta Janar.
Abdullahi jalaluddeen/Kano
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
An sanar da tashin shi daga City kafin karshen kakar wasa ta bana, kuma De Bruyne ya yi bankwana da magoya baya a filin wasa na Etihad bayan wasansa na karshe a gida da suka buga da Bournemouth a watan Mayu, City ta yi kokarin cike gibin da De Bruyne ya bari, yayinda ta dauki yan wasan tsakiya Tijjani Reijnders daga AC Milan da Rayan Cherki daga Lyon.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp