Aminiya:
2025-06-16@04:19:39 GMT

Tinubu ya ba ni riƙon Ribas don wanzar da zaman lafiya — Ibas

Published: 21st, March 2025 GMT

Shugaban Riƙo na Jihar Ribas, Ibok Ibas, ya ce Shugaba Bola Tinubu, ya naɗa shi ne domin dawo da zaman lafiya a jihar, wadda ke fama da rikicin siyasa.

Da yake jawabi a wani shirin talabijin a daren Alhamis a Fatakwal, Ibas ya bayyana naɗin nasa a matsayin matakin da ya dace don kawo ƙarshen rikicin siyasa da ya ɗauki kusan shekaru biyu.

Farashin fetur na iya tashi bayan Dangote ya daina sayar da mai a Naira Muhimman ayyuka 8 a goman ƙarshe na Ramadan

Ya ce rikicin ya hana ci gaban gwamnati, tare da haifar da matsalar tsaro da koma bayan tattalin arziƙi a jihar.

“A matsayina na ɗan yankin Neja Delta, na fahimci damuwar mutanenmu. Rashin tabbas a Jihar Ribas ya shafi iyalai, ’yan kasuwa da rayuwar yau da kullum.

“Naɗin da aka yi min ba na siyasa ba ne, sai dai don dawo da doka da oda, tare da tabbatar da cewa mutanenmu suna rayuwa cikin kwanciyar hankali.”

Ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa babban aikinsa shi ne dawo da zaman lafiya, tabbatar da bin doka da oda, tare da samar da yanayin da zai ba da damar ci gaban gwamnati da bunƙasa tattalin arziƙi.

“Ba aikin mutum ɗaya ba ne. Dole ne al’ummar Ribas su haɗa kai, dattawa, sarakunan gargajiya, ’yan siyasa, ’yan kasuwa, matasa da ƙungiyoyin fararen hula.

“Na zo a matsayin wanda zai hidimta wa jihar, wanda ke da nauyin dawo da zaman lafiya da tsari, domin Jihar Ribas ta dawo da matsayinta na cibiyar arziƙin man fetur a Najeriya.”

Ibas, ya gargaɗi ’yan jihar da su guji tashin hankali da aikata laifuka, inda ya bayyana cewa gwamnati ba za ta yarda da duk wani yunƙuri na kawo ruɗani ba.

Sai dai ya tabbatar da cewa zai mutunta haƙƙoƙin ’yan ƙasa tare da bin doka.

Ya buƙaci jama’a da su haɗa kai don girmama juna da samar da zaman lafiya a jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Naɗi Siyasa Zaman lafiya da zaman lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Rashin aikin yi na daya daga cikin manyan kalubalen da najeriya ke fuskanta a wannan lokaci, musamman la’akari da yanda ake cigaba da samun matasa dake da karfi a jika amma babu aikin yi.

Hukumar kididdiga ta kasa ta fitar da bayanan dake baiyana cewa rashin aikin yi ya karu a najeriya da kaso 5.3 a farkon wannan shekarar, kazalika binciken ya baiyana cewa wadanda basu yi karatu mai zurfi ba sun fi wadanda suka yi karatu mai zurfi samun aikin yi.

NAJERIYA A YAU: 12 Ga Yuni: Me Ranar Dimokuraɗiyya Ke Nufi Ga Talakan Najeriya? DAGA LARABA: Dalilan Rashin Jituwa Tsakanin Marasa Lafiya Da Jami’an Kiwon Lafiya

Wadansu dalilai ne ke kara kawo rashin aikin yi a Najeriya?
Wadansu hanyoyi za’a bi wajen magance rashin aikin yi?
Wadannan da ma wasu tambayoyi na cikin batutuwan da Shirin Najeriya A Yau zai yi duba akai.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • APCn Kaduna Ta Mara Wa Tinubu, Uba Sani Da Kakakin Majalisa Abbas Baya Don Wa’adi Na Biyu
  • Oman ta tabbatar da soke tattaunawar Iran da Amurka zagaye na shida
  • Trump ya dakatar da kamen baƙin haure a wasu wurare na Amurka
  • Wutar lantarki ta kashe mutum 5, ta jikkata 13 a Gombe
  • Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
  • Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu
  • Nijeriya Na Kan Hanyar Farfaɗowar Tattalin Arziki Da Dawo Da Martabar Ƙasa — Ministan Yaɗa Labarai
  • Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung
  • NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A Najeriya