Tinubu ya ba ni riƙon Ribas don wanzar da zaman lafiya — Ibas
Published: 21st, March 2025 GMT
Shugaban Riƙo na Jihar Ribas, Ibok Ibas, ya ce Shugaba Bola Tinubu, ya naɗa shi ne domin dawo da zaman lafiya a jihar, wadda ke fama da rikicin siyasa.
Da yake jawabi a wani shirin talabijin a daren Alhamis a Fatakwal, Ibas ya bayyana naɗin nasa a matsayin matakin da ya dace don kawo ƙarshen rikicin siyasa da ya ɗauki kusan shekaru biyu.
Ya ce rikicin ya hana ci gaban gwamnati, tare da haifar da matsalar tsaro da koma bayan tattalin arziƙi a jihar.
“A matsayina na ɗan yankin Neja Delta, na fahimci damuwar mutanenmu. Rashin tabbas a Jihar Ribas ya shafi iyalai, ’yan kasuwa da rayuwar yau da kullum.
“Naɗin da aka yi min ba na siyasa ba ne, sai dai don dawo da doka da oda, tare da tabbatar da cewa mutanenmu suna rayuwa cikin kwanciyar hankali.”
Ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa babban aikinsa shi ne dawo da zaman lafiya, tabbatar da bin doka da oda, tare da samar da yanayin da zai ba da damar ci gaban gwamnati da bunƙasa tattalin arziƙi.
“Ba aikin mutum ɗaya ba ne. Dole ne al’ummar Ribas su haɗa kai, dattawa, sarakunan gargajiya, ’yan siyasa, ’yan kasuwa, matasa da ƙungiyoyin fararen hula.
“Na zo a matsayin wanda zai hidimta wa jihar, wanda ke da nauyin dawo da zaman lafiya da tsari, domin Jihar Ribas ta dawo da matsayinta na cibiyar arziƙin man fetur a Najeriya.”
Ibas, ya gargaɗi ’yan jihar da su guji tashin hankali da aikata laifuka, inda ya bayyana cewa gwamnati ba za ta yarda da duk wani yunƙuri na kawo ruɗani ba.
Sai dai ya tabbatar da cewa zai mutunta haƙƙoƙin ’yan ƙasa tare da bin doka.
Ya buƙaci jama’a da su haɗa kai don girmama juna da samar da zaman lafiya a jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Naɗi Siyasa Zaman lafiya da zaman lafiya
এছাড়াও পড়ুন:
Faransa ta tabbatar da sa hannunta wajen dakile juyin mulki a Benin
Faransa ta tabbatar da sa hannunta wajen dakile yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin.
Fadar gwammnatin faransa ta Élysée ta ce bisa bukatar hukumomin Benin ta bayar da “goyon baya ta fuskar bayar da bayanai da dabaru” ga sojojin Benin a matsayin martani ga yunkurin juyin mulki da aka dakile a karshen makon da ya gabata.
Sanarwar ta ce Emmanuel Macron ya yi hadin gwiwa” da “musayar bayanai da kasashen yankin,” in ji daya daga cikin masu ba shi shawara ga manema labarai, a cewar AFP.
Shugaban Faransa ya yi magana a ranar Lahadi da takwaransa na Benin, Patrice Talon, wanda sojoji suka nemi su hambarar, da kuma shugaban Najeriya da kuma kasar Saliyo.
Kasar Saliyo ce ke rike da shugabancin kungiyar ECOWAS, wacce ta dauki matakin soja don taimakawa Cotonou wajen dakile yunkurin juyin mulki.
Dama a jiya Shugaban Bola Tinubu ya tabbatar da cewa sojojin kasarsa sun taimaka wajen dakile juyin mulki a benin.
Wata sanarwa da Bayo Onanuga, mai magana da yawun shugaban ya fitar ta ambato Shugaba Tinubu yana cewa “sojojin sun mayar da martani wajen ceto dimokuraɗiyya ta 35.”
Sanarwar ta ce shugaba Tinubu ya dauki mataki bayan samun buƙatar neman ɗauki daga Benin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka RSF : Rabin ‘Yan jarida 67 da aka kashe a bana, a Zirin Gaza ne December 9, 2025 An cire Tony Blair daga jerin wadanda zasu jagoranci Gaza December 9, 2025 Isra’ila ta sake kai hare-haren a kudancin Lebanon December 9, 2025 Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine December 9, 2025 Iran Ta Gudanar Da Taro Kan Yadda Manzon Allah (s) Ya Yi Mu’amala Da Wadanda Ba Musulmi Ba December 9, 2025 Najeriya : Matsala ce ta sa jirgin sojinmu yin saukar gaggawa A Burkina Faso December 9, 2025 Saudiya da Qatar Zasu Gina Layin Dogo Mai Sauri Tsakanin Kasashen Biyu December 9, 2025 Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki December 9, 2025 Pakistan ta Bai Wa Taliban Ta Aghanistan Zabi A Tsakanin Mu’amala Da Ita Ko Da ‘Yan Ta’adda December 9, 2025 Kasashen Iran Da Turkiya Za Su Bunkasa Alakarsu A Fagen Ilimi Da Musayar Fasaha December 9, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci