Kotun ƙoli ta tabbatar da Anyanwu a matsayin sakataren PDP
Published: 21st, March 2025 GMT
Kotun Ƙoli ta yanke hukunci tare da tabbatar da Samuel Anyanwu a matsayin halastaccen Sakataren Jam’iyyar PDP na Ƙasa.
Anyanwu, wanda na hannun daman Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike ne, ya shafe lokaci yana takun-saƙa da Sunday Ude-Okoye kan wannan matsayi.
Tinubu ya ba ni riƙon Ribas don wanzar da zaman lafiya — Ibas Kwankwaso ya yi Allah-wadai da ayyana dokar ta-ɓaci a RibasUde-Okoye ya samu goyon bayan wasu ɓangarori na jam’iyyar PDP bayan Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Enugu ta tabbatar da naɗinsa, biyo bayan hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ta tsige Anyanwu.
Sai dai, a ranar Juma’a, wani kwamitin alƙalan Kotun Ƙoli guda biyar, ya yanke hukunci cewa rikice-rikicen shugabanci a cikin jam’iyya al’amari ne na cikin gida, kuma ba hurumin kotu ba ne sai dai idan akwai wasu dalilai na musamman.
Mai shari’a Jamilu Tukur, wanda ya jagoranci hukuncin, ya bayyana cewa irin wannan shari’a za ta iya shiga hurumin kotu ne kawai idan ta ƙunshi karya doka, aikata laifi, ko saɓa wa yarjejeniya.
Rigima game da muƙamin sakataren jam’iyyar PDP na ƙasa, ta samo asali ne bayan Anyanwu ya ajiye muƙamin don yin takarar gwamna a Jihar Imo, amma bai samu nasara ba.
Yunƙurinsa na sake dawowa kan muƙamin ya jefa jam’iyyar cikin ruɗani.
Bayan Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da tsige shi a watan Disamban 2024, Anyanwu ya shigar da ƙara a Kotun Ƙoli, wacce a yanzu ta yanke hukunci, tare dawo da shi a matsayin halastaccen sakataren jam’iyyar PDP na ƙasa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Anyanwu Sakatare Siyasa jam iyyar PDP tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana
A nasa ɓangaren, mai bai wa Gwamnan Shawara Kan Al’ammuran Tsaro, Janar Dahiru Abdusalam (Mai Ritaya), ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar tana ɗaukar matakai tare da jami’an tsaro don samar da tsaro mai inganci.
Ya kuma bayyana cewa duk da matsalolin tsaro da ake fuskanta a hanyar Damaturu zuwa Gujba, jami’an tsaro na ƙoƙarin yin sintiri domin tabbatar da tsaro.
Janar Dahiru ya ce, “Koda yake muna fuskantar ƙalubale daga Boko Haram a yankunan wasu sansanin sojoji, jami’an tsaro na ci gaba da aikinsu domin kare yankin.”
Ya ƙara da cewa, “Muna taka-tsan-tsan musamman wajen daƙile karɓar haraji daga Boko Haram a wasu yankuna. Wannan al’amari yana da matuƙar wahala, amma muna fatan za mu samu nasara.”
Janar Dahiru ya tabbatar da cewa akwai tsaro a dukkanin sassan jihar tare da haɗin gwiwar sojoji, ‘yansanda, Civilian JTF da ‘yan sa-kai.
Ya kuma bayyana cewa za a fitar da sabbin dabaru cikin makonni masu zuwa domin yaƙar ‘yan ta’adda.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp