Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Yaffa Kusa Da Tel Aviv A Karo Na Biyu A Cikin Sa’o’i 24
Published: 21st, March 2025 GMT
Sojojin kasar Yemen sun cilla makami mai linzami samfurai Balistic kuma Hypersonic kan birnin Yafa kusa da Telaviv a cikin HKI karo na biyu a cikin sa’o’ii 24 da suka gabata. Harin dai yana daga cikin manya-manyan hare-haren da sojojin na Yemen suka kai kan HKI tun bayan sake komawa yaki tufanul Aksa.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kakakin sojojin kasar ta Yemen Burgediya Janar Yahya Saree yana bada sanarwan kai harin, a jiya Alhamis ya kuma kara da cewa, hari mai kyua wanda ya dace da tallafawa Falasdinawa a Gaza.
Saree ya kammala da cewa matukar sojojin HKI sun ci gaba da kissan kiyashin da suke yi a Gaza
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisar Wakilai Ta Gayyaci CBN Da Bankuna Kan Cire Wa Kwastomomi Kudi Ba Dalili
Shagaya ya ce: “Wadannan hanyoyin da bankuna ke amfani da su wajen zaluntar kwastomomi na fiye da kima suna shafar ‘yan kasuwa, masu karamin karfi, dalibai da kuma kungiyoyin da ke cikin mawuyacin hali a wannan yanayin tattalin arziki mai tsanani. Idan ba a gudanar da bincike da daukar mataki cikin gaggawa ba, wannan matsala za ta ci gaba da rage amincewar jama’a ga tsarin banki tare da lalata kokarin shigar da jama’a cikin tsarin hada-hadar kudi.”
Bayan amincewa da kudurin, Majalisar Wakilai ta umurci CBN da ta wallafa jerin caje-cajen da aka amince da su cikin sauki, tare da kakabawa bankunan da suka saba dokoki hukunci mai tsanani.
‘Yan majalisar sun kuma bukaci babban banki ya kafa wata hanyar karbar koke-koke wacce za ta kasance mai saukin amfani da inganci ga kwastomomi da abin ya shafa daga cajin da ba bisa ka’ida ba ko masu yawa.
Haka kuma, Majalisar ta umurci Hukumar Kula da Gasar Kasuwa da Kare Hakkin Masu Amfani (FCCPC) da sauran hukumomin da abin ya shafa da su gudanar da kamfe na wayar da kan jama’a a fadin kasa don ilmantar da ‘yan Nijeria game da hakkokinsu dangane da cajin banki.
An ba kwamitocin da ke kula da Dokokin Banki da Hukumomin Banki aikin gudanar da cikakken bincike tare da mika rahoto cikin makonni hudu don daukar mataki na gaba a majalisa.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA