Gwamna Abdulrazaq Ya Yi Alkawarin Ci Gaba Da Aikin A Kwara
Published: 2nd, May 2025 GMT
Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq ya ce gwamnatinsa ta himmatu wajen gina jihar da ma’aikata za su bunkasa, samar da ayyukan yi masu nagarta, da baiwa kowane bangare damar bayar da gudunmawa mai ma’ana ga ci gaban jihar.
Gwamna AbdulRazaq a cikin sakonsa na bikin ranar ma’aikata ta duniya na shekarar 2025, a Ilorin, ya mika sakon gaisuwa ga maza da mata da jama’a da kungiyoyi masu zaman kansu wadanda kokarinsu ke karfafa tattalin arziki da samar da makomar al’ummarmu.
Ya yaba da gagarumar gudunmawar da ma’aikata ke bayarwa a kowane fanni na sadaukarwa, juriya, da fasaha wanda ya sa su zama ginshiƙan girma da ci gaba.
Gwamnan ya jaddada kudirin gwamnatin na aiwatar da manufofin da za su karfafa ma’aikatan gwamnati, da bunkasa tattalin arziki, da jawo jari, da fadada ayyukan yi.
Ya bayyana cewa, ta hanyar tsare-tsare na samar da ababen more rayuwa da na zamantakewar al’umma, gwamnatin ta tabbatar da daidaiton harkokin kudi, da tabbatar da biyan albashi a kan kari, da tallafa wa harkokin kasuwanci, da samar da hanyoyin kare lafiyar jama’a.
Gwamna AbdulRazaq ya bukaci ma’aikata da su rungumi canji, su inganta nagarta, da kuma yin shiri domin samun damar gobe.
“Ina mika godiya ta ga dukkan ma’aikata saboda muhimmiyar rawar da suka taka a cikin nasarorin da muka samu. Ina kuma yaba wa shugabannin mu na Labour saboda goyon baya da hadin gwiwa.” Ya ce
REL/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jihar Kwara Ta Kafa Kwamitoci 2 Don Tantance Wadanda Suka Yi Ritaya
Daga Ali Muhammad Rabi’u
Gwamnatin Jihar Kwara ta kafa kwamitoci biyu domin tantance bayanan wadanda suka yi ritaya a matakin jiha da kananan hukumomi.
A cikin wata sanarwa da Kwamishinar Kudi ta jihar, Dakta Hauwa Nuru ta fitar, ta bayyana cewa kwamitocin za su tantance tare da tabbatar da sahihancin bayanan wadanda suka yi ritaya, domin a biya su bisa lokacin da suka bar aikin gwamnati.
A cewarta, kwamitin mutum takwas da aka kafa don kula da kudaden ritaya na matakin jiha zai kasance karkashin jagorancin Mai Duba Asusun Jiha, wato (Auditor General), yayin da wanda ke kula da matakin kananan hukumomi zai kasance karkashin Mai Duba Asusun Kananan Hukumomi.
Sanarwar ta bayyana cewa babban burin kwamitocin shi ne tabbatar da cewa an tattara bayanan masu ritaya bisa gaskiya da adalci, tare da biyan su kai tsaye ta asusun ajiyar banki.
Ta kara da cewa, mambobin kwamitocin sun hada da wakilan tsofaffin manyan sakatarorin, kungiyar tsofaffin ma’aikata, Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC), da kungiyar kwadago ta TUC, da sauransu.