Gwamna Abdulrazaq Ya Yi Alkawarin Ci Gaba Da Aikin A Kwara
Published: 2nd, May 2025 GMT
Gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq ya ce gwamnatinsa ta himmatu wajen gina jihar da ma’aikata za su bunkasa, samar da ayyukan yi masu nagarta, da baiwa kowane bangare damar bayar da gudunmawa mai ma’ana ga ci gaban jihar.
Gwamna AbdulRazaq a cikin sakonsa na bikin ranar ma’aikata ta duniya na shekarar 2025, a Ilorin, ya mika sakon gaisuwa ga maza da mata da jama’a da kungiyoyi masu zaman kansu wadanda kokarinsu ke karfafa tattalin arziki da samar da makomar al’ummarmu.
Ya yaba da gagarumar gudunmawar da ma’aikata ke bayarwa a kowane fanni na sadaukarwa, juriya, da fasaha wanda ya sa su zama ginshiƙan girma da ci gaba.
Gwamnan ya jaddada kudirin gwamnatin na aiwatar da manufofin da za su karfafa ma’aikatan gwamnati, da bunkasa tattalin arziki, da jawo jari, da fadada ayyukan yi.
Ya bayyana cewa, ta hanyar tsare-tsare na samar da ababen more rayuwa da na zamantakewar al’umma, gwamnatin ta tabbatar da daidaiton harkokin kudi, da tabbatar da biyan albashi a kan kari, da tallafa wa harkokin kasuwanci, da samar da hanyoyin kare lafiyar jama’a.
Gwamna AbdulRazaq ya bukaci ma’aikata da su rungumi canji, su inganta nagarta, da kuma yin shiri domin samun damar gobe.
“Ina mika godiya ta ga dukkan ma’aikata saboda muhimmiyar rawar da suka taka a cikin nasarorin da muka samu. Ina kuma yaba wa shugabannin mu na Labour saboda goyon baya da hadin gwiwa.” Ya ce
REL/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
SULEJA – An Ci Moriyar Ganga (2)
A gefe guda kuma, al’ummar yankin ne suka sadaukar da gonakinsu, domin amfanin jama’a wajen gina sansanin FCDA. An cimma yarjejeniya cewa; a karshen amfani da filin, za a mayar da shi ga al’umma. Malam Ladan, ya dage har aka tabbatar da wannan yarjejeniya a rubuce kuma Marigayi Abubakar Koko, Sakataren FCDA, ya sa hannu don kada a samu sabanin tarihi.
Amma duk da haka, ba a mika kadarar ba har zuwa shekarar 1987, bayan fafutukar kwato ta tsawon lokaci. Daga bisani kuma, aka mika ta ga kungiyar tsoffin sojoji ta Nijeriya (Nigerian Legion), bayan sun nemi haka. Abin bakin ciki, gwamnatin tarayya ta kara lissafa filin a matsayin daya daga cikin kadarorinta da za a sayar a zamanin mulkin Obasanjo.
Da ba a gano takardun da Marigayi Koko ya sa hannu a kansu daga cikin tsohuwar ajiyar Jihar Neja ba, da an kwace filin. Wannan kuwa sakamakon hangen nesa ne na Malam Ladan.
Bayan dawo da ikon filin a karo na biyu a ranar 30 ga Oktoba, 2007, al’umma suka mika filin ga Gwamnatin Jihar Neja, domin bai wa Jami’ar IBB ta jihar damar kafa reshe a Suleja. Amma fiye da shekara 17 da yin haka, Gwamnatin Neja ta kasa ware ko sisin kwabo don fara gina wannan reshe.
Abin takaici, tun bayan kirkiro Jihar Neja a 1975, babu wata jami’ar gaba da sakandire da gwamnatin jiha ko ta tarayya ta kafa a Masarautar Suleja, duk da koke-koke da dama, har ma da kiran da dan Majalisar Suleja ya yi kwanan nan a gaban majalisar jihar. Wasu sassan na jihar har suna alfahari da dama daga cikin irin wadannan cibiyoyi. Har da shirin kafa makarantar koyon aikin jinya a tsohon wurin makarantar jinya ta FCT a sansanin FCDA ya zama kawai na cin fuska ne kawai. Hakan na faruwa duk da cewa; akwai Cibiyar Lafiya ta Tarayya da aka ware domin Suleja, amma aka karkatar da ita zuwa wani gari a cikin jihar.
Yankin Masarautar Suleja, shi ne mafi tasiri a fannin tattalin arziki a Jihar Neja, saboda kusancinsa da babban birnin tarayya. Gwamnatin Jihar Neja, na ci gaba da cin moriyar hakan ta hanyar tara haraji masu tarin yawa kamar PAYE, kudin filaye da kadarori da sauran haraji. Masarautar Suleja ita kadai na ba da akalla kashi 40 cikin 100 na kudaden da jihar ke samu daga cikin gida. Kudaden harajin da ake tarawa daga Karamar Hukumar Suleja, sun fi na kowace karamar hukuma a jihar. A kwana-kwanan nan, gwamnan ya bayyana haka.
Amma fa, idan aka kwatanta da wasu garuruwa a cikin jihar, ingancin titin da ake ginawa a cikin birnin Suleja, bai kai kima ba ko kadan. Daga Maje zuwa Madalla, ana iya cewa kwangila ce ta biliyoyin Nairori. Amma kuma, babu wani allon kwangila da ke bayyana sunan dan kwangilar ko hukumar da ke sa ido. Wannan yana nuna irin gazawar da ake da ita wajen gaskiya da rikon amana cikin mulki.
Jama’ar Suleja da masu kaunar garin, ba su da wani zabin da ya wuce su saka a ransu cewa; wata boyayyar makarkashiya ce aka shirya, don rage kudin aikin domin amfanuwar wasu. Wannan kuwa, wata shaida ce ta yadda ake yi wa wanda ke kawo riba wulakanci. Abin takaici ne a ce garin da ke bayar da kudaden shiga ya zama wanda aka watsar da shi a fannin gine-gine da walwalar jama’a.
Za a ci gaba In Shaa Allah.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp