Babu ’yan adawan da za su iya hana Tinubu lashe zaɓen 2027 — Ganduje
Published: 21st, March 2025 GMT
Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa babu wata gamayyar ’yan adawa da za ta iya hana Shugaba Bola Ahmed Tinubu lashe wa’adi na biyu a zaɓen 2027.
Ya yi wannan jawabi ne domin mayar da martani ga sabuwar haɗakar ’yan adawa da Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, da wasu shugabanni suka kafa.
A yayin taron manema labarai da Atiku ya gudanar a Abuja a ranar Alhamis, ya soki yadda Tinubu ke tafiyar da mulki, musamman batun ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas.
Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da Tsohon Gwamnan Jihar Imo, Emeka Ihedioha, da wasu ’yan siyasa sun hallara, inda suka bayyana shirin haɗa kai domin karɓe mulki daga hannun Tinubu a 2027.
Sai dai Ganduje ya yi watsi da wannan yunƙuri, inda ya bayyana cewa tafiyar ba za ta yi tasiri ba.
“Babu wata yarjejeniya ko haɗa kai da za ta hana ’yan Najeriya sake zaɓen Tinubu a 2027,” in ji shi a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan wayar da kan jama’a, Cif Oliver Okpala, ya fitar.
Ya ce irin nasarorin da Tinubu ya samu tun bayan hawansa mulki ne zai tabbatar da nasararsa.
“Tabbas Tinubu zai sake lashe zaɓe saboda irin ci gaban da ya kawo tun bayan da ya zama shugaban ƙasa,” in ji Ganduje.
Haka kuma, ya ce wannan sabuwar haɗakar ’yan adawa ba za ta yi tasiri ba, domin ’yan siyasar da ke ciki na da manufofi daban-daban.
“Ku manta da waɗannan tarukan na ‘yan siyasa da maganganunsu marasa tushe, domin yawancinsu ba su da wata makoma ta siyasa,” in ji shi.
“Haɗin gwiwarsu – kama daga kan jam’iyyar LP zuwa PDP da SDP – na ƙunshe da mutanen da ke da ra’ayoyi daban-daban da kuma son zuciya. Ba za su taɓa iya cimma muradi na siyasa ba.”
Wannan martani na Ganduje na nuni da cewa zaɓen 2027 zai kasance mai ɗaukar hankali tare da fafatawa mai zafi tsakanin ɓangarorin siyasa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Adawa adawa Dokar Ta Ɓaci Zaɓen 2027
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Samar Da Manyan Manhajojin AI Sama Da 1500
Kasar Sin ta fitar da manyan manhajojin AI har 1,509, matakin da ya sanya ta kaiwa matsayi na daya cikin jerin sassan duniya da suka fitar da jimillar irin wadannan manhajoji 3,755. Masana na ganin bunkasar sashen masana’antun fasahohin AI na kasar Sin zai ingiza sabbin nasarori a fannin.
A jiya Lahadi, yayin taron karawa juna sani na kasa da kasa game da AI na shekarar 2025, an gudanar da baje kolin nasarori da aka cimma a fannin masana’antun AI na Sin. Kuma a cewar sashen lura da bayanai na cibiyar bincike game da harkokin sadarwa ta Sin, adadin kamfanonin AI na sassa daban daban na duniya ya kai sama da 35,000, yayin da Sin ke da irin wadannan kamfanoni har 5,100, adadin da ya kai kaso 15 bisa dari na jimillar wanda ake da shi a duniya baki daya.
Rahotanni na cewa, adadin masana’antun fannin na ta karuwa ta fuskar kayayyakin more rayuwa, da kayayyakin da yake samarwa domin amfani a masana’antu. Kazalika, akwai jimillar kamfanonin AI masu daraja da yawansu ya kai 271 a duniya baki daya, ciki har da 71 na kasar Sin, adadin da ya kai kaso 26 bisa dari na jimillar wadanda ake da su a duniya. (Mai Fassara: Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp