Aminiya:
2025-06-15@14:39:29 GMT

Babu ’yan adawan da za su iya hana Tinubu lashe zaɓen 2027 — Ganduje

Published: 21st, March 2025 GMT

Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa babu wata gamayyar ’yan adawa da za ta iya hana Shugaba Bola Ahmed Tinubu lashe wa’adi na biyu a zaɓen 2027.

Ya yi wannan jawabi ne domin mayar da martani ga sabuwar haɗakar ’yan adawa da Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, da wasu shugabanni suka kafa.

NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ke Hana Wasu Teloli Cika Alƙawari Majalisar wakilai ta amince da dokar ta-ɓaci a Ribas

A yayin taron manema labarai da Atiku ya gudanar a Abuja a ranar Alhamis, ya soki yadda Tinubu ke tafiyar da mulki, musamman batun ayyana dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas.

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, da Tsohon Gwamnan Jihar Imo, Emeka Ihedioha, da wasu ’yan siyasa sun hallara, inda suka bayyana shirin haɗa kai domin karɓe mulki daga hannun Tinubu a 2027.

Sai dai Ganduje ya yi watsi da wannan yunƙuri, inda ya bayyana cewa tafiyar ba za ta yi tasiri ba.

“Babu wata yarjejeniya ko haɗa kai da za ta hana ’yan Najeriya sake zaɓen Tinubu a 2027,” in ji shi a cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan wayar da kan jama’a, Cif Oliver Okpala, ya fitar.

Ya ce irin nasarorin da Tinubu ya samu tun bayan hawansa mulki ne zai tabbatar da nasararsa.

“Tabbas Tinubu zai sake lashe zaɓe saboda irin ci gaban da ya kawo tun bayan da ya zama shugaban ƙasa,” in ji Ganduje.

Haka kuma, ya ce wannan sabuwar haɗakar ’yan adawa ba za ta yi tasiri ba, domin ’yan siyasar da ke ciki na da manufofi daban-daban.

“Ku manta da waɗannan tarukan na ‘yan siyasa da maganganunsu marasa tushe, domin yawancinsu ba su da wata makoma ta siyasa,” in ji shi.

“Haɗin gwiwarsu – kama daga kan jam’iyyar LP zuwa PDP da SDP – na ƙunshe da mutanen da ke da ra’ayoyi daban-daban da kuma son zuciya. Ba za su taɓa iya cimma muradi na siyasa ba.”

Wannan martani na Ganduje na nuni da cewa zaɓen 2027 zai kasance mai ɗaukar hankali tare da fafatawa mai zafi tsakanin ɓangarorin siyasa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Adawa adawa Dokar Ta Ɓaci Zaɓen 2027

এছাড়াও পড়ুন:

Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila

Jami’in kungiyar Hamas ya bayyana cewa: Kakkausan martanin da Iran ta mayar ya tabbatar da cewa babu mai girman kai da ba zai fuskanci mayar da martani ba

Izzat al-Rishq mamba na ofishin siyasa na kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas ya jaddada cewa: Kakkausan martanin da Iraniyawa suka mayar ya tabbatar da cewa; babu mai girman kai da ba zai fuskanci mayar da martani kan zaluncinsa ba, kuma babu wuce gona da iri ba tare da hukunci ba.

Izzat al-Rishq ya yi nuni da cewa: Tabbas makamai masu linzami da jiragen saman yaki marasa matuka ciki na Iran sun yi nasarar kai wa cikin tsakiyar haramtacciyar kasar Isra’ila, duk kuwa da kace-nacen da ake yi na girke na’urorin kakkabo makamai a haramtacciyar kasar Isra’ila musamman Iron Dome, Arrow da David’s Sling.

Al-Rashq ya kuma bayyana cewa: Tsarin tsaron haramtacciyar kasar Isra’ila ya gaza shawo kan hare-haren da Iran suka kai, kuma a halin yanzu gwamnatin mamayar Isra’ila tana fama da gobarar da ta kunna a tsakanin al’ummomin yankin. A karshe ya jaddada cewa: Sakon a bayyane yake: Duk wanda ya yi tsokana, to tantana kudarsa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda wani ɗan sanda ya rasu a hanyar zuwa ɗaurin aurensa
  • An samu gobara a wasu matatun mai guda biyu na Iran bayan harin da Isra’ila ta kai
  • Arakci: Babu Wani Dalili Na Ci Gaba Da Tattaunawa Tsakanin Iran Da Amurka
  • Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa
  • Gwamnan Kaduna ya bai wa sabon Sarkin Moro’a sandar mulki
  • Jami’in Hamas Ya Jinjinawa Iran Kan Kakkausan Martanin Da Ta Mayar Kan Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • Sarkakiyar Da Ke Tattare Da Zaben 2027 Da Yadda Za Ta Kaya
  • Pogba Na Shirin Komawa Monaco Bayan Dakatar Da Shi
  • Leroy Sane ya koma Galatasaray
  • Iran ta caccaki kudurin IAEA wanda ta ce yana cike da siyasa