Uwargidan Gwamnan Jihar Kaduna, Hajiya Hafsat Uba Sani, ta raba kayan abinci da tufafi ga marayu, mabukata da malamai a Hayin Na’iya dake Kaduna.

An gudanar da taron ne a makarantar Ummul Muminina Hafsat Islamic Academy da ke Hayin Na’iya, Kaduna.

Hajiya Hafsat Uba Sani, wacce Hajiya Aisha Idris Maman ‘Yan Uku ta wakilta, ta jaddada bukatar ganin masu hali su tallafa wa talakawa da mabukata a cikin al’ummarsu.

“Uwargidan gwamnan ta yi imanin cewa marayu da mabukata suna bukatar soyayya, kulawa da tallafi kamar kowane yaro,” in ji ta.

“Wannan shiri ba wai kawai don samar da abinci da tufafi ba ne; yana nufin nuna musu cewa ana kaunarsu kuma ba a manta da su ba.”

“Muna karfafa gwiwar kowa da kowa da ke da hali da ya tallafa wa masu bukata,” ta kara da cewa.

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban makarantar, Malam Hassan Abubakar, ya nuna matukar godiya ga uwargidan gwamnan, Hajiya Hafsat Uba Sani, saboda ci gaba da tallafinta.

Ya bayyana cewa wannan shi ne karo na biyu da take rabon kayan abinci da tufafi ga marayu, mabukata da malamai a makarantar, baya ga hidimar da take yi wa marayu fiye da shekaru goma.

“Fiye da shekaru goma, Uwargidan gwamnan tana daukar dawainiyar marayu, tana samar musu da bukatun rayuwa ba wai abinci da tufafi kawai ba. Wannan shi ne karo na biyu tana kawo wannan tallafi zuwa makarantar mu, kuma ba za mu gaji da gode mata ba,” in ji shi.

“Muna addu’a Allah ya ba ta lafiya da kuma ci gaba, Ya sa mata albarka a cikin ayyukanta,” ya kara da cewa.

Haka nan, shugabar dalibai, Malama Fatima Abdullahi, da daya daga cikin marayun da suka amfana, sun nuna godiyarsu, suna bayyana Hajiya Hafsat a matsayin uwa gare su duka.

Sun yi addu’a Allah ya ci gaba da sa ka mata da alkhairi da kareta.

A yayin taron, an rabawa wadanda suka amfana kayan abinci, zannuwan atamfa da shadda don su more bikin Sallah cikin jin dadi da walwala.

Ci gaba da kokarin jin-kai da Hajiya Hafsat Uba Sani ke yi ya sa ta sami yabo daga jama’a, yana kara tabbatar da jajircewarta wajen inganta rayuwar mabukata a Jihar Kaduna.

 

COV: Khadija Kubau

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kashe makiyaya 2, sun sace shanu 320 a Kaduna

Wasu ’yan bindiga sun kashe wasu makiyaya biyu da suka haɗa da: Mudda Shannon da Suleiman Bello, yayin da suka raunata ɗaya a ƙauyen Kurmin Lemu da ke ƙaramar hukumar Kagarko ta Jihar Kaduna.

Wani ɗan unguwar Kurim Lemu mai suna Shuaibu Ibrahim ya ce, lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 12:07 na tsakar dare.

Ɗalibai sun maƙale lokacin da gini ya rufta suna jarrabawa Ko kwabo ban ciyo bashi ba tun da na zama Gwamnan Kaduna – Uba Sani

Ya ce, ’yan bindigar da suka zo adadi mai yawa tare miyagun makamai sun mamaye sansanin makiyayan inda suka buɗe wuta, inda suka kashe biyu daga cikin makiyayan nan take.

Ya ce, ɗaya daga cikin makiyayan ya tsallake rijiya da baya, amma ya samu raunukan harbin bindiga, inda ya ce ’yan bindigar sun je kai tsaye inda shanun ke da sansani suka kwashe su zuwa cikin dajin.

Ibrahim, ya ce daga baya an kai makiyayin da suka jikkata zuwa asibiti a garin Kagarko, inda yake jinya, kamar yadda ya ce an sanar da sojojin da ke Kagarko.

“An sanar da wasu sojojin da ke Kagarko, tun kafin su isa sansanin ’yan fashin sun tsere da shanun,” in ji shi.

Wani shugaban unguwar yankin da ya nemi a sakaya sunansa, shi ma ya tabbatar wa wakilinmu afkuwar lamarin ta wayar tarho.

Ya ce, ya samu rahoto daga ɗaya daga cikin shugabannin makiyaya na unguwar cewa ’yan bindiga sun kai hari sansanin makiyaya tare da kashe mutum biyu.

“Da safiyar yau ma na samu rahoto daga wani basaraken Fulani daga ƙauyen Kurmin Lemu cewa, wasu ’yan bindiga sun kai hari sansanin makiyaya inda suka kashe wasu Fulani biyu sannan suka yi awon gaba da shanunsu.” In ji shi.

Shugaban Unguwar ya bayyana cewa, ya kuma sanar da sojojin game da harin, duk da cewa ya ce an binne gawarwakin makiyayan biyu da suka mutu.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, ASP Hassan Mansur ya zuwa yanzu bai tabbatar da faruwar lamarin ba, domin har zuwa lokacin da ake haɗa rahoton bai amsa kiran da aka yi masa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan bindiga sun kashe makiyaya 2, sun sace shanu 320 a Kaduna
  • Ko kwabo ban ciyo bashi ba tun da na zama Gwamnan Kaduna – Uba Sani
  • Majalisar Nasarawa Ta Bukaci A Cire Malamai 1000 Daga Aikin Tantancewar Da Ake Yiwa Malamai
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Kulla Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Kasar Indiya Don Habbaka Kiwon Dabbobi
  • Gaza : EU ba ta gamsu da sabon tsarin raba agaji na Amurka da Isra’ila ba  
  • Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai
  • Tashin Hankali A Gaza Bayanda HKI Ta Bude Rumbun Ajiyar Kayakin Agaji A Rafah
  •  Arakci: Idan Birtaniya Ta Ci Gaba Da Batun Dakatar Da Tace Uranium A Iran, Za A Dakatar Da Tattaunawa Da Ita
  • DAGA LARABA: “Sai Na Tara Kudin Cin Abinci Na Nake Iya Siyan Audugar Al’ada”
  • Wata Hajiya ‘Yar Nijeriya Mai Shekaru 75 Ta Rasu A Saudiyya Yayin Aikin Hajji