Uwargidan Gwamnan Jihar Kaduna, Hajiya Hafsat Uba Sani, ta raba kayan abinci da tufafi ga marayu, mabukata da malamai a Hayin Na’iya dake Kaduna.

An gudanar da taron ne a makarantar Ummul Muminina Hafsat Islamic Academy da ke Hayin Na’iya, Kaduna.

Hajiya Hafsat Uba Sani, wacce Hajiya Aisha Idris Maman ‘Yan Uku ta wakilta, ta jaddada bukatar ganin masu hali su tallafa wa talakawa da mabukata a cikin al’ummarsu.

“Uwargidan gwamnan ta yi imanin cewa marayu da mabukata suna bukatar soyayya, kulawa da tallafi kamar kowane yaro,” in ji ta.

“Wannan shiri ba wai kawai don samar da abinci da tufafi ba ne; yana nufin nuna musu cewa ana kaunarsu kuma ba a manta da su ba.”

“Muna karfafa gwiwar kowa da kowa da ke da hali da ya tallafa wa masu bukata,” ta kara da cewa.

Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban makarantar, Malam Hassan Abubakar, ya nuna matukar godiya ga uwargidan gwamnan, Hajiya Hafsat Uba Sani, saboda ci gaba da tallafinta.

Ya bayyana cewa wannan shi ne karo na biyu da take rabon kayan abinci da tufafi ga marayu, mabukata da malamai a makarantar, baya ga hidimar da take yi wa marayu fiye da shekaru goma.

“Fiye da shekaru goma, Uwargidan gwamnan tana daukar dawainiyar marayu, tana samar musu da bukatun rayuwa ba wai abinci da tufafi kawai ba. Wannan shi ne karo na biyu tana kawo wannan tallafi zuwa makarantar mu, kuma ba za mu gaji da gode mata ba,” in ji shi.

“Muna addu’a Allah ya ba ta lafiya da kuma ci gaba, Ya sa mata albarka a cikin ayyukanta,” ya kara da cewa.

Haka nan, shugabar dalibai, Malama Fatima Abdullahi, da daya daga cikin marayun da suka amfana, sun nuna godiyarsu, suna bayyana Hajiya Hafsat a matsayin uwa gare su duka.

Sun yi addu’a Allah ya ci gaba da sa ka mata da alkhairi da kareta.

A yayin taron, an rabawa wadanda suka amfana kayan abinci, zannuwan atamfa da shadda don su more bikin Sallah cikin jin dadi da walwala.

Ci gaba da kokarin jin-kai da Hajiya Hafsat Uba Sani ke yi ya sa ta sami yabo daga jama’a, yana kara tabbatar da jajircewarta wajen inganta rayuwar mabukata a Jihar Kaduna.

 

COV: Khadija Kubau

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

“Bayan karbar mukaminsa na sabon kwamandan hukumar NSCDC na jihar Kano, kwamared Bala Bodinga ya umurci jami’ansa da su sadaukar da kansu ga muhimmin aiki na tabbatar da amincin muhimman kadarori da ababen more rayuwa na kasa.

 

“Kwamandan jihar ya ba da umarnin cewa, ba dare ba rana, cikin sa’o’i 24, dole jami’an hukumar su rika yin sintiri da sanya ido domin dakile ayyukan barayi da masu aikata laifuka a lunguna da sako na jihar,” inji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • An tattauna yadda za a inganta walwalar malamai a Gombe
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • Kundin Bajinta na Guinness ya taya Hilda Baci murna
  • Tattalin Arzikin Sin Ya Samu Ci Gaba Ba Tare Da Tangarda Ba A Watan Agusta
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja