Gwamnatin Yobe na ciyar da almajirai a Tsangayu 85 kullum
Published: 21st, March 2025 GMT
Gwamnatin Jihar Yobe ta kafa cibiyoyin bayar da abinci 85 domin samar wa almajirai abinci a dukkanin Ƙananan Hukumomin 17 na jihar, a lokacin azumin Ramadan.
Sakataren zartarwa na Hukumar Ilimin Larabci da Addinin Musulunci ta Jihar Yobe, Malam Umar Abubakar ne, ya bayyana hakan a wata hira da Daily Trust a ranar Alhamis.
“Muna bai wa makarantun Tsangaya 85 kayan abinci 85, biyar a kowace Ƙaramar Hukuma, inda muke ciyar da almajirai tsakanin 300 zuwa 400 a kowace makaranta,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa Gwamna Mai Mala Buni ne, ya amince da wannan shiri domin tallafa wa yara marasa galihu a jihar.
Baya ga haka, gwamnatin ta buɗe manyan cibiyoyin ciyarwa guda uku a Damaturu domin ciyar da sama da almajirai 2,000 da wasu mabuƙata.
Abubakar, ya bayyana cewa hukumar na kuma samar wa almajiran kayan sakawa.
“Mu na da alhakin tabbatar da cewa waɗannan yara sun ji cewa suna cikin al’umma.
“Zuwa yanzu mun ɗinkawa sama da 850 daga cikinsu tufafi, kuma Insha’Allah, muna da shirin ƙara wannan adadi a nan gaba,” in ji shi.
Ya gode wa gwamnan saboda goyon bayansa tare da kira ga sauran gwamnatoci da masu hali da su taimaka wajen tallafa wa yara marasa ƙarfi a cikin jama’a.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Almajirai ciyarwa gwamnati Tsangaya
এছাড়াও পড়ুন:
Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
Shugaban tawagar baƙin, Alhaji Ibrahim Abdullahi Yar’adua, ya ce sun zo Yobe domin nazarin halin tsaro da tattara bayanai da za su taimaka wajen tsara manufofin tsaron ƙasa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp