Shugaban Kungiyar Manyan Ma’aikatan Jami’o’in Najeriya (SSANU), Comr. Muhammad Haruna Ibrahim ya bukaci gwamnatin jihar Taraba da ta gaggauta biyan ‘yan kungiyar SSANU, jami’ar Jalingo ta jihar Taraba alawus-alawus da suke bi bashi.

 

Comr. Haruna ya yi wannan bukata ne a lokacin da yake jawabi a wajen taron majalisar zartarwa na shiyyar karo na 11 da ya gudana a Jalingo.

 

Shugaban SSANU ya dage cewa ya kamata a yi wa ’ya’yan kungiyar adalci, domin wadanda ba aikin koyarwa ba na daga cikin bangarori hudu da suka kafa jami’a.

 

Sai dai ya yi gargadin cewa kungiyar ba za ta goyi bayan duk wani memba da ya sabawa ka’idojin jami’a ba.

 

Tun da farko, Comr. Bitrus Joseph Ajibauka, shugaban kungiyar TSU reshen, ya yabawa gwamna Agbu Kefas bisa yadda ya amince da biyan wani bangare na bashin albashi da alawus-alawus na kungiyar da kuma aiwatar da sabon mafi karancin albashi na N70,000.

 

JAMILA ABBA

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Taraba

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun ceto fasinjoji 99 daga hatsarin kwale-kwale a Ribas

A ranar Laraba ne jami’an sojojin ruwa na Najeriya da ke Fatakwal suka ceto fasinjoji 99 daga wani hatsarin kwale-kwale da ya rutsa da su a kogin Bukuma da ke ƙaramar hukumar Degema a Jihar Ribas.

Jirgin ruwan, wanda yake na jigilar fasinja yana kan hanyarsa ta daga Fatakwal zuwa Ƙaramar hukumar Akuku-Toru, inda ya yi karo da wani jirgin ruwa a tsakiyar kogin.

Gobara ta lalata shagunan kasuwar waya a Kwara Dalilin da ya sa aka samu fashewar abubuwa a barikin Maiduguri – Sojoji

Jami’ar yaɗa labarai na sansanin, Laftanar Kwamanda Bridget Bebia, a wata sanarwa da ta fitar a Fatakwal, ta ruwaito Kwamandan sojojin masu aikin bincike, Commodore Cajethan Aniaku, ya tabbatar da faruwar lamarin.

A cewar Aniaku, ba a samu asarar rai ba, kuma an kuɓutar da akasarin kayayyakin fasinjojin tare da ceto su daga cikin jirgin.

Rundunar sojin ruwan ta ce jami’anta da ke NSS 035 tare da tallafin jiragen ruwa huɗu sun ƙaddamar da aikin bincike mai inganci, inda suka yi nasarar ceto dukkan fasinjoji 99.

“Saboda saurin agajin da tawagar ceto ta yi, ba a sami asarar rayuka ko jikkata ba,” in ji Rundunar Sojan Ruwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HOTUNA: Yadda aka tarbi Shugaba Tinubu a Katsina
  • NLC Kano Ta Yabawa Gwamnati Na Kokarin Kyautata Jin Dadin Ma’aikata
  • Zamfara Ta Biya Sama Da Naira Biliyan 13 A Matsayin Bashin Garatuti Da Aka Gada – Mataimakin Gwamna.
  • Gwamnan Kabawa Ya Tabbatarwa Ma’aikatan Gwamnati Ingantacciyar Walwala
  • ’Yan acaba sun yi wa mai fura fyaɗe Abuja
  • Ma’aikata Sun Kauracewa Fareti, Sun Gudanar Da Taron Goyon Baya Ga Dakataccen Gwamnan Ribas
  • Sojoji sun ceto fasinjoji 99 daga hatsarin kwale-kwale a Ribas
  • Dubban Mutanen Burkina Faso Sun Yi  Gangamin Nuna Goyon Bayan Shugaban Kasa Ibrahim Traore
  • Tinubu zai ziyarci Katsina