Shugaban Kungiyar Manyan Ma’aikatan Jami’o’in Najeriya (SSANU), Comr. Muhammad Haruna Ibrahim ya bukaci gwamnatin jihar Taraba da ta gaggauta biyan ‘yan kungiyar SSANU, jami’ar Jalingo ta jihar Taraba alawus-alawus da suke bi bashi.

 

Comr. Haruna ya yi wannan bukata ne a lokacin da yake jawabi a wajen taron majalisar zartarwa na shiyyar karo na 11 da ya gudana a Jalingo.

 

Shugaban SSANU ya dage cewa ya kamata a yi wa ’ya’yan kungiyar adalci, domin wadanda ba aikin koyarwa ba na daga cikin bangarori hudu da suka kafa jami’a.

 

Sai dai ya yi gargadin cewa kungiyar ba za ta goyi bayan duk wani memba da ya sabawa ka’idojin jami’a ba.

 

Tun da farko, Comr. Bitrus Joseph Ajibauka, shugaban kungiyar TSU reshen, ya yabawa gwamna Agbu Kefas bisa yadda ya amince da biyan wani bangare na bashin albashi da alawus-alawus na kungiyar da kuma aiwatar da sabon mafi karancin albashi na N70,000.

 

JAMILA ABBA

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Taraba

এছাড়াও পড়ুন:

Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga

Wani yaro mai kimanin shekaru goma a duniya ya harbe mahaifinsa wanda jami’in ɗan sanda ne mai mukamin sufeto a Jihar Anambra da ke kudu maso gabashin Nijeriya.

Haka kuma, wakilinmu ya ruwaito cewa yaron ya harbi wani yayansa da bindigar mahaifin nasa ta aiki kirar AK-47.

Kashe jagoran addini na Iran zai kawo ƙarshen yaƙi — Netanyahu Mun bankaɗo sabuwar dabarar ’yan siyasa ta satar kuɗi — EFCC

Wannan dai na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Anambra, Tochukwu Ikenga ya raba wa manema labarai a ranar Litinin.

Kakakin ya ce an gaggauta kai jamin asibiti domin a ceto rayuwarsa amma likitoci suka tabbatar da cewa rai ya riga ya yi halinsa.

Sanarwar ta ce “a ranar Lahadi 15 ga watan Yuni, dan gidan wani jami’in dan sanda mai kimanin shekara goma da haihuwa ya harbe mahaifinsa har lahira ya kuma jiwa yayan sa mummunan rauni.

“Abin bakin ciki muna sanar da ku mutuwar jami’inmu mai mukamin sufeto, Okolie Amechi, bisa harbe shi da dansa ya yi a gidansa.

“Wannan ba karamin abin takaici ba ne da kaddara,” in ji sanarwar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Wani Basarake
  • Dan shekara 10 ya harbe mahaifinsa ɗan sanda a Anambra
  • Dan shekara 10 ya kashe mahaifinsa ɗan sanda da bindiga
  • Masu Garkuwa Da Mutane Sun Dira Jihar Kogi, Sun Sace Mutane 1
  • Tinubu zai je jaje bayan kisan fiye da mutum 100 a Benuwe
  • Tinubu ya bayar da umarnin binciken hare-haren Benuwe
  • Tinubu ya bayar umarnin binciken hare-haren Benuwe
  • An tallafa wa mata 250 da abinci da kayan sana’a a Kaduna
  • Harin Benuwe: ’Yan sanda sun tarwatsa masu zanga-zanga
  • Masu ƙwacen waya sun kashe ma’aikacin Jami’ar Northwest a Kano