Araghchi : Iran za ta mayar da amsa ga wasikar Trump cikin kwanaki masu zuwa
Published: 21st, March 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya bayyana cewa, Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta mayar da martani ga wasikar shugaban Amurka Donald Trump a cikin kwanaki masu zuwa ta hanyoyin da suka dace.
Araghchi ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi kai tsaye a gidan talabijin na Jamhuriyar Musulunci ta Iran (IRIB) jiya Alhamis.
Araghchi ya kuma lura cewa a wannan karon, ci gaban ya zo tare da wani yunkuri na diflomasiyya daga Amurkawa, ciki har da wasika da bukatar yin shawarwari.
Ya kuma bayyana cewa manufar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a bayyane take. “Ba za mu shiga tattaunawa kai tsaye karkashin matsin lamba, barazana, ko karin takunkumi.”
A cewar Araghchi, tilas ne a gudanar da shawarwari bisa daidaito da kuma kyakkyawan yanayi.
Ministan harkokin wajen kasar ya kuma bayyana cewa wasikar “mafi yawan barazana ce,” amma kuma akwai damamaki a ciki.
“Mun yi nazari sosai kan dukkan bangarorin wasikar, tare da yin la’akari da kowane daki-daki sosai,” in ji shi.
A farkon watan Maris ne Trump ya bayyana cewa ya rubuta wasika zuwa ga Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei.
A karshen watan Fabrairu, Ayatullah Khamenei, a wata ganawa da jami’an sojin sama a Tehran, ya bayyana cewa bai ga amfanin tattaunawa da Amurka saboda ba zata warware matsaloli ba.
Kalaman nasa sun zo ne sa’o’i bayan da gwamnatin ta Trump ta kakaba wa Iran takunkumai da Trump ya bayayana da “mafi girman matsin lamba” kan Iran.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: bayyana cewa
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila ta kaddamar da hare-hare kan yankuna da dama na Iran ciki har da Tehran
Isra’ila ta kaddamar da hare hare kan wasu gine-gine da cibiyoyi a sassa daban daban na Iran ciki har da Tehran babban birni a cikin daren jiya wayewar wannan safiya ta Juma’a.
Kafofin yada labarai na Iran sun ce akwai mata da yara da dama daga cikin wadanda suka yi shahada a hare-haren.
An kuma bayar da rahoton kai hari a wurare a Natanz, Khorramabad, da Khondab, da dai sauransu.
Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce harin da Isra’ila ta kai wa Iran zai kai tsawon kwanaki idab akwai bukatar hakan.
“Za a ci gaba da gudanar da wannan aiki na tsawon kwanaki kamar yadda ake tsara don kawar da wannan barazanar,” in ji Netanyahu a cikin wata sanarwa ta bidiyo.
Hare-haren da sojojin gwamnatin sahyoniyawan suka kai kan Tehran ya yi sanadiyar shahadar wasu fitattun masana kimiyyar nukiliya na Iran, Mohammad Mahdi Tehranchi da Fereydoon Abbasi, dama wasu fararen hula.
Tehranchi shi ne shugaban jami’ar Azad ta Musulunci ta Iran.
Fereydoon Abbasi ya kasance tsohon shugaban hukumar makamashin nukiliya ta Iran.
An dakatar da zirga-zirgar jiragai a filin jirgin saman Imam Khumaini na Tehran.
Harin ya zo ne kwanaki biyu gabanin wani sabon zagaye na shawarwarin nukiliyar Iran da Amurka.