HausaTv:
2025-12-10@18:29:41 GMT

Araghchi : Iran za ta mayar da amsa ga wasikar Trump cikin kwanaki masu zuwa

Published: 21st, March 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya bayyana cewa, Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta mayar da martani ga wasikar shugaban Amurka Donald Trump a cikin kwanaki masu zuwa ta hanyoyin da suka dace.

Araghchi ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi kai tsaye a gidan talabijin na Jamhuriyar Musulunci ta Iran (IRIB) jiya Alhamis.

Araghchi ya kuma lura cewa a wannan karon, ci gaban ya zo tare da wani yunkuri na diflomasiyya daga Amurkawa, ciki har da wasika da bukatar yin shawarwari.

Ya kuma bayyana cewa manufar Jamhuriyar Musulunci ta Iran a bayyane take. “Ba za mu shiga tattaunawa kai tsaye karkashin matsin lamba, barazana, ko karin takunkumi.”

A cewar Araghchi, tilas ne a gudanar da shawarwari bisa daidaito da kuma kyakkyawan yanayi.

Ministan harkokin wajen kasar ya kuma bayyana cewa wasikar “mafi yawan barazana ce,” amma kuma akwai damamaki a ciki.

“Mun yi nazari sosai kan dukkan bangarorin wasikar, tare da yin la’akari da kowane daki-daki sosai,” in ji shi.

A farkon watan Maris ne Trump ya bayyana cewa ya rubuta wasika zuwa ga Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei.

A karshen watan Fabrairu, Ayatullah Khamenei, a wata ganawa da jami’an sojin sama a Tehran, ya bayyana cewa bai ga amfanin tattaunawa da Amurka saboda ba zata warware matsaloli ba.

Kalaman nasa sun zo ne sa’o’i bayan da gwamnatin ta Trump ta kakaba wa Iran takunkumai da Trump ya bayayana  da “mafi girman matsin lamba” kan Iran.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: bayyana cewa

এছাড়াও পড়ুন:

Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta

Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) ta ayyana dokar ta-baci a yankin, kwana biyu bayan yunkurin juyin mulki da bai yi nasara ba a kasar Jamhuriyar Benin.

Shugaban Hukumar ECOWAS, Omar Touray, ne ya sanar da haka a yayin zaman majalisar tsaro ta hukumar karo na 55 a Abua.

Touray ya ce daukar matakin ya zama dole domin shawo kan barazanar da juyin mulki ke wa tsarin dimokuradiyya a yankin, wanda ke bukatar matakan zuba jari na gagagwa domin tabbatar da tsaron al’umma.

A yayin jawabinsa ga ministoci da manyan jami’an gwamnati da ke halartar taron, ya bayyana yadda yawaitar samun juyin mulki  a Yammacin Afirka ke barazana ga tsaro da zaman lafiya a yankin.

Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato HOTUNA: Yadda dalibai 100 da aka sace a Neja suka dawo

Ya ce, “Babban barazana ga yankinmu sun haɗa da ci gaba da katsalandan na sojoji (kamar yadda aka gani kwanan nan a Guinea-Bissau da Jamhuriyar Benin); rashin bin ka’idojin sauyin mulki a Guinea inda shugaban soja ke ƙoƙarin zama farar hula; raguwar damar shiga zabe a ƙasashe da dama; ƙara karfin ’yan ta’adda, kungiyoyi masu laifi da ke dauke da makamai; da kuma matsin lamba na siyasar duniya da ke shafar diflomasiyya da haɗin kan ƙasashen mambobi.”

Touray ya jaddada cewa “zabe ya zama babban abin da ke tayar da rikici a cikin al’ummarmu.”

Ya kuma ambaci yunƙurin juyin mulki da aka yi kwanan nan da tattaunawa da ƙasashen AES (Burkina Faso, Mali da Nijar) da suka fice daga ECOWAS, yana mai nanata bukatar gaggawa ta haɗin gwiwar yankin wajen yaki da ta’addanci da laifukan da ke ketare iyaka.

Ya bayyana lamarin a matsayin abin da bai taɓa faruwa ba, yana gargadi da cewa, “Idan aka dubi wannan hali, ya dace mu bayyana cewa al’ummarmu tana cikin yanayin gaggawa.”

Touray ya bukaci a riƙa yin taron Majalisar Sulhu da Tsaro akai-akai a shekara mai zuwa, yana mai cewa ECOWAS dole ta “haɗa ƙarfi da ƙarfi don fuskantar barazanar ta’addanci da ’yan fashi, waɗanda ba sa mutunta iyakokin ƙasashe.”

Ya kuma bayyana muhimman wuraren da ministoci za su riƙa kula da su, ciki har da rikicin Guinea-Bissau, tafiyar da sauyin mulki, magance ƙara yawaitar cire mutane daga siyasa, da kuma kare haɗin kan yankin daga matsin lamba na waje.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • Ministan Makamashi: Iran Tana Da Sanayya Ta Ilimi Na Samar Da Hadari Domin Yin Ruwan Sama
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
  • Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima
  • Juyin Mulki: ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a kasashenta
  • Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine
  • Ecowas Ta Tura Sojoji Zuwa Jamhuriyar Benin Don Dakile Juyin Mulki
  • IRGC: Makaman Iran Sun Fada Kan Matatan Man Haifa Har Sau Biyu A Yakin Kwanaki 12
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin