Leadership News Hausa:
2025-05-21@20:33:23 GMT

Bukatar Kawo Karshen Mamayar Da Kamaru Ke Yi Wa Yankunan Nijeriya

Published: 18th, April 2025 GMT

Bukatar Kawo Karshen Mamayar Da Kamaru Ke Yi Wa Yankunan Nijeriya

Akwai kuma Sanata Adeniyi Adegbonire dan jam’iyyar APC daga mazabar Ondo ta tsakiya, Sanata Seriake Dickson dan jami’yyar PDP, daga mazabar Bayelsa ta Gabas, Sanata Shehu Lawan Kaka, dan jam’iyyar APC, daga mazabar Borno ta tsakiya.

Sauran sun hada da; Sanata Banigo Ipaligo dan jam’iyyar PDP, daga mazabar Ribas ta Yamma, Sanata Jarigbe Jarigbe dan jami’yyar PDP, daga Koros Riba ta Arewa, Sanata Ekong Sampson dan jami’yyar PDP, daga mazabar Akwa Ibom ta Kudu, Sanata Sani Bello dan jami’yyarAPC, daga mazabar Neja ta Arewa sai kuma Sanata Aniekan Bassey, dan jam’iyyar PDP, daga mazabar Akwa Ibom.

Majalisar ta kafa wannan kwamtin ne, biyo bayan kudurin da Sanata Aniekan Bassey na mazabar Arewa da Gabas daga Akwa Ibom, ya gabatar mata wacce ta yi daidai da dokokin 41 da 51.

Bugu da kari, a cikin kudurin da Sanata Bassey ya gabatar wa da Majalisar Dattawan ya yi gargadi da cewa, kutsen na ‘yan ta’addar daga kasar Kamaru, zai iya shafar tattalin arzikin jihar ta Akwa Ibom

Sanatan ya shedawa Majalisar cewa, yankin na Efiat, da ke a karamar hukumar Mbo a Akwa Ibom, na daga cikin yankin da aka bai wa kasar Kamaru a shekarar 1913, biyo bayan yarjejeniyar Anglo-German ko kuma a hukuncin da yarjejeniyar Babban Kotun Koli ta Duniya Duniya ta yanke a watan Okutobar 2002.

A nan, muna jinjiawa Majalisar ta Dattawa bisa kafa wannan kwamtin mai mambi tara, musamman domin kwamitin ya gudanar da bincike, kan wannan batun, na zargin kutsen ‘yan ta’addar na kasar Kamaru,a wannan yankin.

Sai dai, a wannan lokacin, yana da kyau a ci gaba da tsimayin sakamakon binciken da kuma shawarwarin da kwamtitin zai gabatar wa da Majalisar ta Dattawa kan wannan batun, domin sanin mataki na gaba da za a dauka.

Batu na maganar rikicin kasa, akasari, yana da wuyar lamari, wajen warware wa, musamman duba da cewa, Nijeriya da kasar Kamaru, kasashe ne, da suka gaji iyakoin kasa daga turawan mulkin mallaka, wadanda kuma, tun a baya, ba a fayyace yadda suke ba.

Bugu da kari, wannan lamari ne, mai matukar mahimmanci da ya shafi kasar nan.

Kazalika, ya zama waji, ‘yan Nijeriya su hada kansu, domin kare iyakokin kasar ga dukkan wata barazana, da za ta iya shafar kasar.

Sai dai, damuwar da akasarin ‘yan Nijeriya ke ci gaba da nunawa kan batun shi ne, na rashin mayar da hankali a siyasance, domin lalubo da mafita kan lamari irin wannan.

Mu a nan, muna kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kasance mai sanya ido sosai da kuma daukar kwararan matakai da za su kasance ba su kai ga zubar da kimar Nijeriya a idon duniya ba, wajen kare yiwa tattalin arzikin kasar nan.

Hakazalika, ya zama wajbi, Nijeriya ta tashi tsaye, wajen kare kasar daga dukkan wani na’ui na barazana daga kere domin kare kasar nan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kamaru Mamaya Nijeriya dan jam iyyar daga mazabar kasar Kamaru

এছাড়াও পড়ুন:

Zulum zai saya wa sojoji da ’yan sa-kai ƙarin motoci don yaƙar Boko Haram

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya amince da sayen ƙarin motoci guda 10 don taimaka wa sojoji da ’yan sa-kai wajen yaƙi da ’yan Boko Haram da ISWAP.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin wata ziyara da ya kai Kala-Balge, inda ya gana da ƙungiyoyi daban-daban.

An kashe makiyaya 2 a wani hari a Filato Yadda ’yan sanda suka kashe dan fashi suka kwato bindigogi 7 a Abuja

Ya ce za a bai wa ’yan sa-kai motoci shida ƙirar Toyota Hilux, ciki har da CJTF, mafarauta da ’yan banga, sannan za a bai wa sojoji ƙarin motoci huɗu masu bindiga.

Zulum, ya kuma raba wa iyalai 10,000 da ke fama da talauci a yankin kayan abinci, yawancin waɗanda suka samu kayan mata da marasa galihu ne.

A garin Rann, hedikwatar Ƙaramar Hukumar Kala-Balge, gwamnan ya kwana a can tare da duba lafiyar jami’an tsaro da kuma tallafa musu.

Zulum, ya ce ziyarar tana cikin ƙoƙarinsa na ƙarfafa haɗin kai da juriya a tsakanin al’ummar jihar, duba da ƙalubalen tsaro da suke fuskanta daga ‘yan ta’addan Boko Haram da ISWAP.

Ya ce, “Ina kira ga dukkanin mazauna Borno da su haɗa kai da jami’an tsaro domin kare mu daga barazanar tsaro.”

Zulum, ya kuma nuna godiyarsa ga al’ummar jihar da sauran yankuna da suka amsa kiran yin azumi da addu’a domin samun zaman lafiya.

Ya ce mutane daga wasu jihohi da ma ƙasashen waje sun haɗa kai da su wajen neman taimakon Allah domin kawo ƙarshen matsalar tsaro.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hajji: NAHCON Ta Kammala Jigilar Kashi 77 Na Mahajjatan Nijeriya Zuwa Saudiyya 
  • Jigajigan Jihar Kebbi Sun Bukaci Hadin Kan ‘Ya’yan Jam’iyyar APC
  • Jagora: Jamhuriyar Musulunci Ba Ta Bukatar Izinin Wani Mahaluki Domin Tace Sanadarin Uranium
  • Zulum zai saya wa sojoji da ’yan sa-kai ƙarin motoci don yaƙar Boko Haram
  • Hare-Haren Wuce Gona Da Irin Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa
  • NiDCOM Ta Ceto ‘Yan Nijeriya 13 Da Aka Yi Safarar Zuwa Ghana Da Mali
  • Hajji: Kawo Yanzu An Kammala Jigilar Maniyyatan Jihohi 12 A Nijeriya – NAHCON
  • Iran Ta Ce Gabatar Da Bukatar Dakatar Da Tashe Makamashin Uranium Karshen Tattaunawar Da Amurka
  • Fahimtar Hakikanin kasar Sin
  • Mataimakiyar shugaban majalisar dokokin Edo ta yi murabus