Matan da suka tsira daga Boko Haram na buƙatar tallafin musamman
Published: 18th, April 2025 GMT
Mata da ’yan mata da suka tsira daga tashin hankalin ‘yan Boko Haram a Arewa Maso Gabashin Nijeriya na fuskantar matsaloli masu yawa, ciki har da shiga tsananin damuwa da fuskantar nuna wariya da rashin samun dama na neman kuɗi da kuma uwa-uba rashin samun kulawar gwamnati da na al’umma.
A lokacin tashin hankali da yaƙe-yaƙe mata da yara ne suka fi shan wahala sosai daga munanan hare-haren da ke shafar lafiyar jikinsu da ta ƙwaƙwalwarsu, sannan sun fi kowa faɗawa matsalar tattalin arziƙi da shiga cikin ɗimuwa.
Tun farkon fara rikicin Boko Haram a watan Yulin 2009, mata da yara a Arewa Maso Gabas sun kasance cikin waɗanda aka aka fi ci wa zarafi. Yawancinsu a kan tilasta musu shiga yaƙi inda ake amfani da su a matsayin ‘yan ƙunar baƙin wake, ko a yi amfani da su a matsayin garkuwa.
Da yawansu sun rasa rayukansu, wasu an ci zarafinsu ta hanyar fyaɗe, sannan kuma an hana su damar ci gaba da neman ilimi. Har ila yau, an sace ɗaruruwansu kuma aka yi amfani da su tamkar bayi.
Fiye da mata miliyan biyu da ƙanana yara sun rasa matsugunansu, inda aka tilasta musu tserewa zuwa sansanonin ‘yan gudun hijira ko wurare da ba su san su ba.
A cikin sansanonin ‘yan gudun hijira, yawancin ‘yan mata ba su samu kulawa da buƙatunsu na asali ba wanda hakan ya sa aka yi ta amfani da su ta hanyar yi musu fyaɗe ana ba su kayan tallafi ko abinci.
Yayin da gwamnatin Nijeriya ke samun nasara kan Boko Haram sannu a hankali, wata hanya mai amfani da ake gani don gina zaman lafiya mai ɗorewa a Arewa Maso Gabas ita ce ta hanyar bai wa mata damar samun ci gaba a rayuwarsu.
Mata da yaran da suka tsira daga hare-haren Boko Haram na buƙatar isasshen tallafi don sake farfaɗo da rayuwarsu. Hakan zai taimake su wajen yin aiki tuƙuru da bayar da gudunmawarsu wajen gina zaman lafiya da ci gaban ƙasa.
Hauwa Bello, ‘yar shekaru 65 wacce aka fi sani da Falmata daga garin Gwoza, ta bayar da labarin irin wahalhalun da ta fuskanta a ƙarƙashin ikon Boko Haram. “Ba zan taɓa mantawa da ranar da Boko Haram suka kama Gwoza ba. Wannan ce ranar ƙarshe da na ga ‘ya’yana maza guda biyu,” in ji Falmata.
Ta bayyana yadda mutane suka firgita lokacin da Boko Haram suka shigo garin Gwoza suna ta harbe-harbe, lamarin da ya sa mutane suka fara gudu cikin a firgeci. Duk da gargaɗin da ta yi wa ‘ya’yanta maza bai hana sun fita daga gida cikin ruɗani ba kuma daga nan aka kashe su.
Bayan watanni shidda a ƙarƙashin ikon Boko Haram a garin Gwoza, Boko Haram sun sanar da su cewa sun samu labari mai tushe cewa Sojojin Nijeriya na kan hanyar zuwa don su sake ƙwace garin Gwoza daga hannunsu, don haka suka ce ya zama dole su gudu su bar garin. Falmata, da aka tilasta ta tsere tare da su, ta kwashe watanni ukku a cikin daji kafin ta tsere tare da wasu mata da ƙananan yara.
Sun yi tafiya tsawon kwanaki kafin sojojin Nijeriya suka same su inda suka kai su Sansanin Barikin soja na Giwa Army Barracks a Maiduguri.
Falmata ta kuma bayyana wahalhalun da ta sha a sansanin tare da sauran ‘yan gudun hijira.
“Rayuwa a sansanin da ke a bariki akwai wahala sosai. Da farko mun samu taimako da kulawa sosai, amma daga baya sai aka yi watsi aka manta da mu. A wasu lokutta sai mun sha wahala wajen samun abinci sau ɗaya a rana, kuma babu magani ga duk waɗanda suka kamu da rashin lafiya.”
Mijin Falmata ya mutu ne sakamakon rashin kulawa da shi daga zazzaɓin cizon sauro da ba a yi masa magani ba. Ala tilas ta bar sansanin inda ta tsere zuwa Abuja tare da ɗanta guda ɗaya da ya rage. “A wannan shekarun nawa da irin yanayin lafiyata, ba zan iya yin aiki ba. Ɗana ne kaɗai mai kula da mu, kuma yana buƙatar tallafi da damar ci gaba don ya iya kula da mu.”
Falmata Garba, wata matashiya da ta sha wahala a hannun Boko Haram, ta bayyana wa wakilinmu irin yadda ta yi rayuwa da su.
“Sun sace mu ne daga garin Gwoza suka kai mu cikin daji,” in ji Falmata.
Ta ƙara da cewa, “an tilasta mini auren wani daga cikinsu, duk da yake mun haifi yara biyu da shi, amma dukkan yaran sun rasu saboda yunwa da rashin magani.”
A lokacin da ta yanke shawarar tserewa, Falmata ta shirya da wasu yara suka bi dare suka sulale. Sun yi amfani da damar da suka samu ta cewa ’Yan Boko Haram ɗin da suke tsare da su sun fita kai hari wani gari sannan suka tsere, inda suka kwana ukku suna tafiya cikin jeji. Daga bisani sun haɗu da rundunar sojan Nijeriya wacce ta kai su Maiduguri.
“Amma yanzu gamnati ta kore mu, sun ce mana mu kwashe yanamu-yanamu mu bar sansanin ’yan gudun hijirar, kuma tun daga wannan lokacin na faɗa tasku. A halin yanzu ina tsaka mai wuya kuma ina neman agaji don in samu in tsira da raina,” In ji Falmata Garba.
Ita ma Hauwa Hamman Gwoza, wata matashiya ‘yar shekara 26, ta ba da labarin abin da ta fuskanta a ƙarƙashin ikon Boko Haram a garin Gwoza. Karatunta ya tsaya cak lokacin da Boko Haram suka mamaye garin, suka ƙona makarantu sannnan suka hana su samun damar yin karatu.
Hauwa an tilasta mata zama a gida tsawon watanni, tana tsoron hukunci ko auren dole idan aka kama ta a waje. Lokacin da Boko Haram suka bar Gwoza, Hauwa ta kasance tare da iyayenta inda aka tilasta su shiga daji tare da mayaƙan Boko Haram. Bayan wasu watanni, ta samu ta tsere, amma ‘yan’uwanta mata biyu suna can tare da Boko Haram, an tilasta musu yin aure da mayaƙan tare da haifar musu yara.
Bayan ta tsere ne ta samu ta yi aure, amma mijinta ya bar ta bayan ta haifi yara huɗu. Yanzu tana zaune ne tare da ɗan’uwanta a sansanin ‘yan gudun hijira na Bwari a Abuja. Hauwa ta yi kira ga gwamnatin tarayya da ta taimaka mata ta fara kasuwanci domin kula da ‘ya’yanta.
“Kamar yadda kuke gani, ba ni da wata hanyar samun kuɗin shiga sai dai ɗinkin hula da nake yi da hannu, wanda yake ɗaukar kusan wata biyu kafin in kammala guda ɗaya. Ina kira ga gwamnatin tarayya da hukumomin da abin ya shafa da su taimake ni da jari ko horo na ƙwarewa don in dogara da kaina in kula da yarana.”
A cikin watan Nuwambar bara, Ƙungiyar Kare Haƙƙin bil’Adam ta Amnesty International ta ƙaddamar da wani shiri mai taken #EmpowerOurGirls da nufin jawo hankalin hukumomin Nijeria da sauran masu ruwa da tsaki don tallafa wa mata da ƙananan yaran da suka tsira daga musgunawar ’yan Boko Haram da ta soja a jihohin Arewa maso Gabas don su dogara da kansu.
Daraktan Ƙungiyar Kare Haƙƙin bil’Adam ta Amnesty International a Nijeriya, Isah Sanusi, ya tabbatar wa Aminiya fara aiatar da wannan kamfe tare da yin alƙawarin bayar da cikakken bayani game da shirye-shiryen Amnesty International ke yi don ganin an ba wa mata da ‘yan matan da suka tsira daga Boko Haram tallafin da ya dace.
Sanata Ireagbor, Masanin Tsaro kuma Mai ba da Shawara kan Harkokin Tsaro a Nijeriya ya bayyana cewa, bai wa mata da ‘yan mata da suka tsira daga hare-haren mayaƙan Boko Haram damar samun ayyukan yi da tallafin kuɗi ba kawai wajibi ba ne, wata dabara ce ta yaƙi da ayyukan ta’addanci da a Arewa baki ɗaya.
“Ta hanyar bai wa waɗannan mutanen damar kula da kansu da iyalansu, za mu iya rage tasirin manufofin ‘yan ta’adda waɗanda sau da yawa ke amfani da halin talaucin da mutane ke ciki don yaɗa manufofinsu a cikin al’umma da kuma samun sabbin masu shiga ƙungiyarsu,” in ji Ireagbor.
Ya ƙara da cewa, “a wannan yanayin, matan da aka bai wa dama za su iya zama wakilan sauyi wajen inganta zaman lafiya da daidaito tsakanin maza da mata, da kuma juriya a cikin al’ummominsu.
”Haɗin kai tare da shugabannin al’umma da ƙungiyoyin mata yana da muhimmanci don tabbatar da cewa shirye-shiryen sun dace da al’adun al’umma kuma suna magance ƙalubalen da waɗanda abin ya shafa ɗin ke fuskanta.”
Naomi Abwaku Chibok, Jami’ar Hulɗa da Jama’a na Hukumar Raya Arewa Maso Gabas (NEDC), ta bayyana wa wakilinmu cewa, hukumar tana yin iyakar ƙoƙarinta don tabbatar da cewa mata da ‘yan matan da suka tsira daga Boko Haram a Arewa Maso Gabas ana kula da su da kuma basu damar sake gina rayuwarsu.
“Tare da ƙoƙarin da hukumar ke yi wajen taimakawa matan da suka tsira daga musgunawar Boko Haram ko ta soja, an kafa cibiyar koyon sana’o’i a Ningi Jihar Bauchi. Inda waɗanda abin ya shafa musamman mata suke koyon sabbin hanyoyin sana’a tare da ƙwarewar da za su iya tallafawa rayuwarsu.
“NEDC ta kuma kafa Ɗakin Tiyata don kula da matsalar Yoyon-fitsari ga mata da ke buƙatar hakan,” in ji Naomi.
Da muka tuntuɓe ta, ta hanyar manhajar WhatsApp, Kwamishiniyar Harkokin Mata da Ci gaban Jama’a ta Jihar Borno, Hajiya Zuwaira Gambo, ta bayyana cewa ba za ta iya yin tsokaci ba saboda yanayin lafiyarta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram matan da suka tsira daga da Boko Haram suka a Arewa Maso Gabas yan gudun hijira a garin Gwoza Boko Haram a a rayuwarsu
এছাড়াও পড়ুন:
Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115
115-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissiso da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin dastane rastan, ko kum littafin mathnawi na maulana Jalaluddeen rumi. Ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu na yau.
///… Masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-hassan limami na biyu daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s), kuma da na farko ga Fatimah(s) diyar manzon All..(s), sannan jikansa na farko.
A cikin shirimmu da ya gabata, mun ji yadda wasu malaman tarihi suka kawo wasu hadisai wadanda basu inganta ba suka jinginawa Imam Alhassan Almujtaba (a) dangane da son da yakewa khalifa na ukku wasu Uthman bin Affan, mun gudanar da bincike cikin daya daga cikin hadisan a sanadi da kuma mataninsa inda muka tabbatar da cewa , Mada’ini wanda aka ruwaito wannan hadisin, nasibi ne, wato wata jama’a wacce ta ke addini da kiyayya ga iyalan gidan manzon All..(s), har’ila yau yana kirkiro hadisan na kariya ya jinganawa manzon All..(s) na muzantasu da kuma kirkiro wasu hadisan daga manzon All..(s) na yabon banu umayya.
Sannan a matanin hadisin mun bayyana kariyar zance mai cewa Imam Hassan yana zargin babansa Imam Ali (a) da hannu a kashe Uthman dan Affan, sannan yana tare da mahaifinsa, manya-manyan yake-yake guda biyu da yayi a lokacin khalifancinsa, da wadanda suke tuhumarsa da zubar da jinin Khalifa Uthman.
Wato yake-yaken Jamal da Siffin. Imam Hassan (a) ya yaki wadannan makiyan mahaifinsa wadanda suke zarginsa da hannu a kissan Uthman. Kuma bamu taba sanin akwai sabani tsakanin Imam Ali (a) da yayansa Alhassan da Alhussain (a).
Daga karshen mun kawo maku yadda manyamanayn sahabban manzon All..(s) da suka rage a Madina suka rubuta wasi ku zuwa sauran sahabbansa a sauran yankuna na daular musulunci suna neman taimakonsu don kauda Khalifa uthman daga khalifanci, saboda ya sabawa littafin All..da sunnar manzon All..da kuma siran khalifofin da suka gabata. Sun koka kan yadda ya mika al-amuran daular musulunci ga danginsa banu Umayya suna satar dukiyar al-umma sannan sun barsu da talauci.
Mun bayyana cewa akwai abubun lura a cikin wannan wasikar kamar haka,
1-Sunan zarginsa na kin amfani da littafin All..
02-Sauya sunnan manzon All..(s) da kuma, yayi watsi da ita,
03-yayi watsi ga hanyar khalifofin biyu da suka gabace shi wato Abubakar da Umar
04- Ya kauda ma’anar khalifancin manzon All..(s) daga yadda yakamata ta kasance,
5-Kwace dukkan duniyar Al-ammu da kuka sarrafata a wasu wurare kebantattu, wato kashe ta kan dangin khalifa wato Banu Umayya.
Malaman tarihi sun bayyana cewa, wadannan al-amura sun girgiza daular musulunci, kuma sun kusan su rusata.
Sannan mun bayyana cewa wadanda suke sukan shugabancin Khalifa Uthman sun rubuta wata wasika ga murabiduna, wato wadanda suke kula da kan iyakokin daular musulunci daga cikin sahabbai, sun bukacesu su dawo madina don tsada khalifancin manzon All..(a), don tabbatar da khaifancin ya dawo kan yadda yakamata ya kasanci.
Ga kuma matanin wasikar kamar haka.
{Lalle ku, kun fita ne don ku yi jihadi a kan tafarkin All..mai girma da daukaka, kuna neman kare addinin Muhammad (s) to lalle khalifanku ya lalata addnin Muhammadu, ku dawo ku tsaida shi,…}.
Banda haka a lokacinda wasikun nan suka isa yankuna da dama na daular musulunci sun yi ta aika tawaga don ganin abinda yake faruwa a Madina, sannan tawagogi da suka isa Madina don ganewa idanunsu abubuwan da suke faruwa, da kuma tattauna matsalolin da kuma yadda za’a magance su, sun hada da.
Tawaga daga kasar Masar, kafin haka akwai mutane 700 da suka tura tun farko bayan da suka kama wani bawan Khalifa Uthman wanda ake kira warsh dauke da wasikar Khalifa zuwa dan uwansa gwamnan Masar Abdullahi ibn Abisharkh, na ya kashe sui dan sun isa da sabon kwamna Muhammad dan Abubakar.
A wannan karon mutanen masar sun aiki mutane 400. Tare da jagorancin Muhammad dan Abubakar wanda dama yana manina, da Abdrrahman dan Udais Al-balawi.
2-sai tawagar Kufa wanda ya hada da Malik dan Ashtar, Zaidu dan Sauhan Al-Abdi, da Ziyad dan Annadhir Al-harithy. Da abdullahi dan Asam Al-Amuri da shugabansu gaba daya, Amru dan Ah-tham .
03-sai tawagar Basra wacce ta hada da Hakin dan Jibilah, tere da wasu mutane 100. Bayan haka wasu khamsin sun bisu. A cikinsu akwai Zarih dan Abidi Al-Abdi, da bishru dan shuraih Alkaisi, da dan Mahrash, da wasunsu daga cikin fitattun mutane kuma sanannu na Basra.
A lokacinda wadannan tawagogi suka isa Madina an yi maraba da su, kuma nag ode masu da karban kiran da aka yi masu, sannan sun tattauna da sauran sahabbai da kuma musulmai dan al-amuran da suka faru, da kuma irin mummunan halin da musulmi suka shiga ciki saboda yadda Khalifa Uthman ya sauya al-amura da dama, daga cikin ya hanasu dukiyoyinsu, wadanda suka saba samu a zamanin khalifofin da suka gabata. Ko kuma ya fita daga tsarin da manzon All..(s) yake raba dukiya a cikin al-umma.
Bayan yan kwanaki sai mutanen kasar masar sun ga cewa kafin ko me da farko a rubutawa khalifa Usman wasika, a yi masa nisiha kan ya dawo kan tafarkin da ya dace ga kuma kadan daga cikin abinda wasikar ta kunsa.
Bayan Basmala da salati ga manzon All..(s) da kuma godiya ga All..sai suka ce
(bayan haka, ka sani kan cewa, {Lalle All..baya sauya halin da mutane suke ciki sai sai sun sauya halinsu, muna hadaka da All..kuma muna sake hadaka da All..Lalle kai kana cikin duniya mai gucewa, … .. kuma kada ka manta da rabon a lahira, kada duniya ta rudeka, kuma ka san cewa mu don All..muke yi, kuma don All…muke fushi. Kuma muna neman yardarm All.. ne, kuma lalle ba zamu dauke takubbammu daga wuyoyimmu ba saika tuba daga abubuwan da ka aikata mana, tuba mai tsanani kuma a fili, wannan shi ne maganarmu da kai, sannan bukatarmu a gareka, All..ne mai karban uzurimmu dangane da kai..wassalam…}.
A lokacinda Khalifa Uthman ya karanta sai ya ji tsoro. Sai Mughira ya nemi izininsa yayi Magana da mutane, sai ya bashi izini, a lokacinda suka ganshi sai suka daga murya suna cewa: Ya makaho koma ya Fajiri koma ya fasiki koma.ya koma ya kasa Magana da su.
Sai Uthman ya kira Amru dan Asi, ya bukaci yayi Magana da su, ya amince, amma a lokacinda suka ganshi, sai yayi masu, sallama ba wanda ya amsa daga cikinsu, suka daga murya suna cewa: Ko koma ya makiyin All.. ka kuma ya dan Nabigha. Kai ba amintecce ne a wajemmu ba kuma mai aminci ba.
A nan sai Khalifa Uthman ya fahinci cewa babu wanda zai taimaka masa sai Amirulminina Aliyu dan Abitalib (a), sai ya nemi taimakonsa, ya fada masa cewa, yayi kira ga mutane zuwa ga Alkur’ani mai girma da sunnar annabinsa.
Sai Imam ya amince, amma da sharudda kan cewa, ya yi masa alkawali tsakaninsa da All..zai yi aiki da abinda ya fada. Sai ya yi alkawali zai zai cika alkawalinsa, za iyi aiki da abinda ya fada.
Sai Imam (a) ya je wajen mutane, shima a lokacinda suka ganshi suka ce, koma , sai yace a’a na zo maku da cewa, za’a yi aiki da littafin All.., kuma za’a sauya duk abinda kuka yi fushi dominsa. Sai ya fada masu abinda khlifa ya bada. Sai suka ce: Ka lamunce mana haka zai faru? Sai yace :ee. Sai suka ce mun yarda.
Sai ya shigar da manya manya daga fitattun mutane wajen Uthman, sai suka yi ta sukansa, sannan suka ce, ya Sanya abinda ya yi alkawali na aiki da littafin All..da kuma sunnar manzon All..(s) da kuma bawa musulmi hakkinsu da ake basu.
Sai ya amince ya rubuta ya basu sannan suka karbi takardan suka kama hanyar masar.
Wannan shi ne nassin abinda ya rubuta ya basu’
{Wannan rubutun daga bawan All..Uthman Amirulmuminina zuwa ga wadanda suke sukansa daga cikin muminai da musulmai, kan cewa hakkinsu ne in yi aiki da littafin All..da sunnar annabinsa a cikinu, za’a bawa talaka hakkinsa, wanda yake cikin tsoro a amintar da shi, wanda aka kora adawo da shi …kuma za’a samar da kudade ga musulmi. Sannan Aliyu dan Abitalib (a) shi ne mai lamuncewa muminai, kuma wajibi ne ga Uthman ya cika alkawalin da ya dauka cikin wannan rubutun}.
Banda haka Zubair dan Awwam, Talha dan Ubaidullahi,Sa’du dan Abi wallas, Abdullahi dan Umar, Zaidu dan Thabit, Sahal dan Hunaif,, Abu ayyuba Khalid dan zaid, kuma anyi wannan rubutun a cikin watan Zulkida shekara ta shekara 35.
Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu. Wassalau alaikum warahamatullahi wa barakathu.