Tarayyar Afirka Tana Shiga Tsakanin Bangarorin Dake Rikici Da Juna A Kasar Sudan Ta Kudu
Published: 3rd, April 2025 GMT
Wakilan kungiyar tarayyar Afirka sun isa birnin Juba na kasar Sudan ta Kudu, a kokarin da suke yi na shiga tsakanin hana komawa yakin basasa.
Tarayyar Afirkan ta fara kokarin shiga tsakani ne, bayan daurin talala da aka yi wa mataimakin shugaban kasa Riek Machar a gidansa,lamarin da ya sake jefa kasar cikin zaman dar-dar.
Gwamnatin Salva Kir tana zargin Machar da cewa yana rura wutar wani sabon yaki a cikin kasar. A ranar Laraba ta makon da ya shude ne dai aka yi wa mataimakin shugaban kasar daurin talala a gidansa saboda fadan da ake yi a yankin Upper Nile tsakanin sojojin gwamnati da kuma masu dauke da makamai na rundunar “White Army”.
A lokacin yakin basasar da kasar ta fuskanta a tsakanin 2013 zuwa 2018, an yi kawance a tsakanin mayakan “White Army” da kuma rundunar Machar, sai dai a wannan lokacin mataimakin shugaban kasar ya karyata cewa yana da alaka da abinda yake faruwa.
Tawagar tarayyar Afirkan da ta isa birnin Juba ta kunshi majalisar dattijan nahiyar Afirka, da ta kunshi tsohon shugaban kasar Burundu, Domitien Ndayizeye da kuma tsohon alkali daga kasar Kenta Effie Owuor.
A ranar Litinin din da ta gabata maid a tsohon shugaban kasar Kenya Fira ministan Kenya Raila Odinga ya isa birnin na Juba, a madadin kungiyar kasashen gabashin nahiyar Afirka.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Larijani Ya Gana Da Firai ministan Kasar Iraki A Bagdaza
Babban sakataren majalisar koli ta tsaron kasar Iran, Dr Ali Larijani ya gana da firai ministan kasar Iraki Mohammad Shia Assudani a birnin bagdaza inda bangarorin biyu suka tattauna al-amura da dama da suka shafi harkokin tsaro a tsakanin kasashen biyu da kuma matsalolin yankin wadanda suka hada da kasar falasdinu.
Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar iran ya bayyana cewa Dr Larijani ya gana da shugaban kasar ta Iraki Abdullataf Rashid da kuma Qasin al-araji mai bawa shugaban kasa shawara a kan al-amuran tsaron kasa.
A gaban shugaban kasan ne Larijani da Araji suka rattaba hannu kan wata sabuwar yarjeniyar tsaro mai muhimmanci tsakanin kasashen biyu.
Dr larijani ya yabawa kasar Iran a kokarinda take yi don tabbatar da zaman lafiya da tsaro a cikin kasar, ya kuma yadda ake gudanar da zirayar 40 na Imam Hussain (a) a kasar, inda miliyoyin mutane daga ko ina suke shigowa kasar don ziyarar.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Mafi yawan Kasashen Duniya Sun Amince Da Samarda Kasar Falasdinu August 11, 2025 Mahukuntan Iraki Sun Bayyana Cewa: Akwai Yiwuwar Masu Ziyarar Arba’een Na Imam Husaini {a.s} Zasu Zarce Miliyan 4 August 11, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun kai Wasu Munanan Hare-Hare Kan Yankunan Zirin Gaza August 11, 2025 Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Gudanar Da Zaman Taro Kan Aniyar ‘Yan Sahayoniyya Kan Gaza August 11, 2025 Shugaban Iran: Dole ne duniya ta kawo karshen laifukan yakin Isra’ila a Gaza August 11, 2025 Israila Ta Kashe ‘Yan Jarida 4 A Harin Da Ta Kai Kan Tantinsu A Gaza August 11, 2025 Iran: Ba a yanke wani abu game da tattaunawa da Washington ba August 11, 2025 Kwamitin Tsaro ya yi zaman gaggawa kan Shirin Isra’ila na mamaye Gaza August 11, 2025 Iraki: An bankado wani yunkurin kai wa masu ziyarar Arbaeen hari August 11, 2025 Chadi: An Daure Wani Dan Adawa Shekaru 20 A Gidan Kaso Da tara August 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci