Tarayyar Afirka Tana Shiga Tsakanin Bangarorin Dake Rikici Da Juna A Kasar Sudan Ta Kudu
Published: 3rd, April 2025 GMT
Wakilan kungiyar tarayyar Afirka sun isa birnin Juba na kasar Sudan ta Kudu, a kokarin da suke yi na shiga tsakanin hana komawa yakin basasa.
Tarayyar Afirkan ta fara kokarin shiga tsakani ne, bayan daurin talala da aka yi wa mataimakin shugaban kasa Riek Machar a gidansa,lamarin da ya sake jefa kasar cikin zaman dar-dar.
Gwamnatin Salva Kir tana zargin Machar da cewa yana rura wutar wani sabon yaki a cikin kasar. A ranar Laraba ta makon da ya shude ne dai aka yi wa mataimakin shugaban kasar daurin talala a gidansa saboda fadan da ake yi a yankin Upper Nile tsakanin sojojin gwamnati da kuma masu dauke da makamai na rundunar “White Army”.
A lokacin yakin basasar da kasar ta fuskanta a tsakanin 2013 zuwa 2018, an yi kawance a tsakanin mayakan “White Army” da kuma rundunar Machar, sai dai a wannan lokacin mataimakin shugaban kasar ya karyata cewa yana da alaka da abinda yake faruwa.
Tawagar tarayyar Afirkan da ta isa birnin Juba ta kunshi majalisar dattijan nahiyar Afirka, da ta kunshi tsohon shugaban kasar Burundu, Domitien Ndayizeye da kuma tsohon alkali daga kasar Kenta Effie Owuor.
A ranar Litinin din da ta gabata maid a tsohon shugaban kasar Kenya Fira ministan Kenya Raila Odinga ya isa birnin na Juba, a madadin kungiyar kasashen gabashin nahiyar Afirka.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung
A wannan rana, a gun taron manema labarai da aka gudanar bayan kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC, Lee Jae-myung ya ce hadin gwiwar tattalin arziki tsakanin Sin da Koriya ta Kudu yana da matukar muhimmanci, ya kuma yi imanin cewa birnin Shenzhen na kasar Sin zai karbi bakuncin kwarya-kwaryar taron shugabannin kungiyar APEC cikin nasara a shekara mai zuwa.(Safiyah Ma)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA